< 1 Samuel 27 >
1 David disait en son cœur: « Je vais maintenant périr un jour par la main de Saül. Il n'y a rien de mieux pour moi que de m'échapper dans le pays des Philistins; et Saül désespérera de moi, pour me chercher encore dans tout le territoire d'Israël. Je m'échapperai donc de sa main. »
Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Wata rana Shawulu zai kashe ni, abu mafi kyau da zan yi shi ne in tsere zuwa ƙasar Filistiyawa. Da haka Shawulu zai fid da zuciya ga nemana a ƙasar Isra’ila, a can kuwa zan tsira daga hannunsa.”
2 David se leva et passa, lui et les six cents hommes qui étaient avec lui, chez Akish, fils de Maoch, roi de Gath.
Sai Dawuda tare da mutanensa, mutum ɗari shida suka tashi suka haye zuwa wurin Akish ɗan Mawok, sarkin Gat.
3 David habitait avec Akish à Gath, lui et ses hommes, chacun avec sa maison, même David avec ses deux femmes, Ahinoam la Jizreelite et Abigaïl la Carmélite, femme de Nabal.
Dawuda da mutanensa suka zauna a Gat tare da Akish. Kowa ya kasance tare da iyalinsa. Dawuda kuwa yana tare da matansa biyu. Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel matar Nabal da ya mutu daga Karmel.
4 Saül apprit que David s'était enfui à Gath, et il cessa de le chercher.
Da Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya gudu zuwa Gat, bai ƙara fita nemansa ba.
5 David dit à Akish: « Si maintenant j'ai trouvé grâce à tes yeux, qu'on me donne une place dans une des villes du pays, pour que j'y demeure. Car pourquoi ton serviteur devrait-il habiter avec toi dans la ville royale? »
Sai Dawuda ya ce wa Akish, “In na sami tagomashi a gabanka ka ba ni wani wuri a cikin biranenka in zauna a can. Don me bawanka zai kasance tare da kai a gidan sarauta?”
6 Et Akish lui donna Ziklag ce jour-là: c'est pourquoi Ziklag appartient aux rois de Juda jusqu'à ce jour.
A ranar Akish ya ba shi Ziklag wanda tun dā take ta sarkin Yahuda.
7 Le nombre de jours que David vécut dans le pays des Philistins fut d'une année entière et de quatre mois.
Dawuda ya zauna a yankin Filistiyawa shekara ɗaya da wata huɗu.
8 David et ses hommes montèrent et attaquèrent les Gueshuriens, les Girziens et les Amalécites, car c'étaient les habitants du pays d'autrefois, sur le chemin de Shur, jusqu'au pays d'Égypte.
Dawuda da mutanensa suka haura suka yaƙi Geshurawa, da Girziyawa, da Amalekawa. (Waɗannan su ne mazaunan ƙasar a dā, tun daga Shur har zuwa ƙasar Masar.)
9 David frappa le pays, ne sauva ni homme ni femme en vie, et prit les brebis, les bœufs, les ânes, les chameaux et les vêtements. Il s'en retourna, et arriva chez Akish.
Duk lokacin da ya yaƙi wani wuri, ba ya barin namiji ko mace da rai, amma sai ya kwashe tumaki, da shanu, da jakuna, da raƙuma, da riguna, sa’an nan yă koma wurin Akish.
10 Akish dit: « Contre qui as-tu fait un raid aujourd'hui? » David répondit: « Contre le midi de Juda, contre le midi des Jerahmeelites, et contre le midi des Kenites. »
Idan Akish ya ce, “Ina ka kai hari yau?” Sai Dawuda yă ce, “Na kai hari a Negeb ta Yahuda, ko Negeb ta Yerameyel, ko Negeb na Keniyawa.”
11 David ne sauva ni homme ni femme en vie pour les amener à Gath, en disant: « De peur qu'on ne raconte à notre sujet: « David a fait cela, et c'est ainsi qu'il a agi tout le temps qu'il a vécu au pays des Philistins ». »
Bai bar a kawo namiji ko mace da rai a Gat ba, gama yana tunani, “Za su ba da sanarwa a kanmu su ce, ‘Ga abin da Dawuda ya yi.’” Haka ya yi ta yi dukan rayuwarsa a ƙasar Filistiyawa.
12 Akish crut David, en disant: « Il a rendu son peuple d'Israël complètement odieux. C'est pourquoi il sera mon serviteur pour toujours. »
Akish ya amince da Dawuda sosai, har ya ce wa kansa, “Ga shi ya mai da kansa abin ƙi ga mutanensa Isra’ilawa, zai zama bawana har abada.”