< 1 Samuel 24 >
1 Lorsque Saül revint de la poursuite des Philistins, on lui dit: « Voici David dans le désert d'En Gedi. »
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Saül prit alors trois mille hommes d'élite de tout Israël et alla chercher David et ses hommes sur les rochers des chèvres sauvages.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 Il arriva aux bergeries qui se trouvaient sur le chemin, où il y avait une grotte; et Saül y entra pour se soulager. Or, David et ses hommes se tenaient dans les profondeurs de la caverne.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 Les hommes de David lui dirent: « Voici le jour dont Yahvé t'a parlé: « Voici que je livre ton ennemi entre tes mains, et tu lui feras ce qui te semblera bon. » David se leva alors et coupa en secret le pan de la robe de Saül.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 Par la suite, le cœur de David le frappa parce qu'il avait coupé le pan de la robe de Saül.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 Il dit à ses hommes: « L'Éternel interdit que je fasse cela à mon seigneur, l'oint de l'Éternel, que j'étende ma main contre lui, puisqu'il est l'oint de l'Éternel. »
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 David vérifia ses hommes par ces paroles et ne leur permit pas de se lever contre Saül. Saül se leva de la caverne et poursuivit son chemin.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Après cela, David se leva aussi, sortit de la caverne et cria après Saül: « Mon seigneur le roi! » Lorsque Saül regarda derrière lui, David s'inclina, le visage tourné vers la terre, en signe de respect.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 David dit à Saül: « Pourquoi écoutes-tu les paroles des hommes qui disent: « Voici que David cherche à te faire du mal? »
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 Voici, tes yeux ont vu aujourd'hui comment Yahvé t'a livré entre mes mains dans la caverne. Certains m'ont incité à te tuer, mais je t'ai épargné. J'ai dit: « Je n'étendrai pas ma main contre mon seigneur, car il est l'oint de l'Éternel ».
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 D'ailleurs, mon père, voici, oui, voyez le pan de votre robe dans ma main; car en ce que j'ai coupé le pan de votre robe et ne vous ai pas tué, sachez et voyez qu'il n'y a ni mal ni désobéissance dans ma main. Je n'ai pas péché contre toi, bien que tu aies chassé ma vie pour la prendre.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 Que Yahvé juge entre moi et toi, et que Yahvé me venge de toi, mais ma main ne sera pas sur toi.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 Comme le dit le proverbe des anciens: « Du méchant sort la méchanceté »; mais ma main ne sera pas sur toi.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 Contre qui le roi d'Israël est-il sorti? Qui poursuivez-vous? Un chien mort? Une puce?
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 Que Yahvé soit donc juge, qu'il prononce la sentence entre moi et toi, qu'il voie, qu'il plaide ma cause, et qu'il me délivre de ta main. »
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 Lorsque David eut achevé de dire ces paroles à Saül, ce dernier dit: « Est-ce là ta voix, mon fils David? » Saül éleva la voix et pleura.
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 Il dit à David: « Tu es plus juste que moi, car tu m'as fait du bien, tandis que je t'ai fait du mal.
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 Tu as déclaré aujourd'hui que tu m'avais bien traité, car lorsque Yahvé m'a livré entre tes mains, tu ne m'as pas tué.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 Car si un homme trouve son ennemi, le laissera-t-il partir indemne? Que l'Éternel te récompense donc bien pour ce que tu m'as fait aujourd'hui.
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 Maintenant, voici, je sais que tu seras roi et que le royaume d'Israël sera établi entre tes mains.
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Jure-moi donc maintenant par Yahvé que tu n'extermineras pas ma descendance après moi, et que tu ne détruiras pas mon nom de la maison de mon père. »
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 David fit un serment à Saül. Saül rentra chez lui, mais David et ses hommes montèrent à la forteresse.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.