< 1 Samuel 22 >

1 David partit donc de là et se réfugia dans la caverne d'Adullam. Ses frères et toute la maison de son père l'apprirent, et ils descendirent auprès de lui.
Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
2 Tous ceux qui étaient dans la détresse, tous ceux qui avaient des dettes et tous ceux qui étaient mécontents se rassemblèrent auprès de lui, et il devint leur chef. Il y avait avec lui environ quatre cents hommes.
Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
3 David se rendit de là à Mitspé de Moab, et il dit au roi de Moab: « Laisse sortir vers toi mon père et ma mère, jusqu'à ce que je sache ce que Dieu fera pour moi. »
Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
4 Il les amena devant le roi de Moab, et ils habitèrent avec lui tout le temps que David fut dans la forteresse.
Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
5 Le prophète Gad dit à David: « Ne reste pas dans la forteresse. Pars, et va dans le pays de Juda. » David partit, et arriva dans la forêt de Hereth.
Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
6 Saül apprit que David avait été découvert, avec les hommes qui étaient avec lui. Saül était assis à Guibea, sous le tamaris de Rama, sa lance à la main, et tous ses serviteurs se tenaient autour de lui.
Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
7 Saül dit à ses serviteurs qui se tenaient autour de lui: « Écoutez, Benjamites! Le fils de Jessé donnera-t-il à chacun de vous des champs et des vignes? Vous établira-t-il tous chefs de milliers et chefs de centaines?
Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
8 Est-ce pour cela que vous avez tous conspiré contre moi, et qu'il n'y a personne qui me dise que mon fils a conclu un traité avec le fils d'Isaï, et qu'il n'y a aucun d'entre vous qui ait pitié de moi, ou qui me dise que mon fils a excité mon serviteur contre moi, pour le mettre à l'affût, comme c'est le cas aujourd'hui? »
Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
9 Alors Doëg, l'Edomite, qui se tenait près des serviteurs de Saül, prit la parole et dit: « J'ai vu le fils d'Isaï venir à Nob, chez Ahimélec, fils d'Ahitub.
Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
10 Il a consulté Yahvé à son sujet, lui a donné à manger et lui a remis l'épée de Goliath le Philistin. »
Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
11 Alors le roi envoya appeler le prêtre Achimélec, fils d'Achitub, et toute la maison de son père, les prêtres qui étaient à Nob; et ils vinrent tous auprès du roi.
Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
12 Saül dit: « Écoute maintenant, fils d'Achitub. » Il a répondu: « Me voici, mon seigneur. »
Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
13 Saül lui dit: « Pourquoi avez-vous conspiré contre moi, vous et le fils d'Isaï, en lui donnant du pain et une épée, et en demandant à Dieu pour lui, afin qu'il se lève contre moi, pour me guetter, comme il le fait aujourd'hui? »
Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
14 Achimélec prit la parole devant le roi et dit: « Qui, parmi tous tes serviteurs, est aussi fidèle que David, gendre du roi, chef de ta garde et honoré dans ta maison?
Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
15 Ai-je aujourd'hui commencé à demander à Dieu de le faire? Que cela soit loin de moi! Que le roi n'impute rien à son serviteur, ni à toute la maison de mon père, car ton serviteur n'a rien su de tout cela, ni en moins ni en plus. »
A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
16 Le roi dit: « Tu mourras, Achimélec, toi et toute la maison de ton père. »
Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
17 Le roi dit aux gardes qui se tenaient autour de lui: « Tournez et tuez les prêtres de l'Éternel, car leur main est aussi avec David, et parce qu'ils savaient qu'il s'était enfui et ne me l'ont pas révélé. » Mais les serviteurs du roi ne voulurent pas étendre leur main pour tomber sur les prêtres de Yahvé.
Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
18 Le roi dit à Dœg: « Retourne-toi et attaque les prêtres! » Dœg, l'Edomite, se retourna et attaqua les prêtres, et il tua en ce jour quatre-vingt-cinq personnes qui portaient un éphod de lin.
Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
19 Il frappa Nob, la ville des prêtres, du tranchant de l'épée: hommes et femmes, enfants et nourrissons, bétail, ânes et moutons, du tranchant de l'épée.
Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
20 L'un des fils d'Ahimélec, fils d'Ahitub, nommé Abiathar, s'échappa et s'enfuit après David.
Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
21 Abiathar raconta à David que Saül avait tué les prêtres de l'Éternel.
Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
22 David dit à Abiathar: « Je savais que ce jour-là, lorsque Dœg l'Édomite était là, il ne manquerait pas de dire à Saül. Je suis responsable de la mort de toutes les personnes de la maison de ton père.
Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
23 Reste avec moi. N'aie pas peur, car celui qui cherche ma vie cherche ta vie. Tu seras en sécurité avec moi. »
Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”

< 1 Samuel 22 >