< 1 Samuel 19 >

1 Saül parla à Jonathan, son fils, et à tous ses serviteurs, pour qu'ils fassent mourir David. Mais Jonathan, fils de Saül, se réjouissait beaucoup de David.
Shawulu ya gaya wa ɗansa Yonatan da ma’aikatansa su kashe Dawuda. Amma Yonatan yana son Dawuda sosai.
2 Jonathan dit à David: « Saül, mon père, cherche à te tuer. Prends donc soin de toi dès le matin, vis dans un lieu secret et cache-toi.
Sai ya gargaɗe shi ya ce, “Mahaifina Shawulu yana neman hanyar da zai kashe ka. Ka kula da kanka gobe da safe, ka tafi wani wuri ka ɓuya.
3 Je sortirai et je me tiendrai près de mon père dans le champ où tu es, et je parlerai de toi à mon père; et si je vois quelque chose, je te le dirai. »
Zan je in tsaya da mahaifina a fili inda kake, zan yi masa magana game da kai. Zan kuma gaya maka abin da na ji.”
4 Jonathan parla en bien de David à Saül, son père, et lui dit: « Que le roi ne pèche pas contre son serviteur, contre David, car il n'a pas péché contre toi, et parce que ses œuvres ont été très bonnes à ton égard;
Yonatan ya yi magana mai kyau a kan Dawuda a wajen mahaifinsa ya ce, “Kada sarki yă yi wani mummunan abu wa bawansa Dawuda, gama bai yi maka wani abu marar kyau ba. Abin da ya yi ya amfane ka ƙwarai da gaske.
5 car il a mis sa vie en main et a frappé le Philistin, et Yahvé a remporté une grande victoire pour tout Israël. Vous l'avez vu et vous vous êtes réjouis. Pourquoi donc voulez-vous pécher contre le sang innocent, pour tuer David sans cause? »
Ya yi kasai da ransa sa’ad da ya kashe Bafilistin nan. Ubangiji ya ba wa dukan Isra’ila babban nasara, ka gani, ka kuma yi farin ciki. Don me za ka ci mutuncin amintaccen mutum kamar Dawuda ta wurin kashe shi ba tare da wani dalili ba?”
6 Saül écouta la voix de Jonathan, et Saül jura: « L'Éternel est vivant, il ne sera pas mis à mort. »
Shawulu ya saurari Yonatan sai ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a kashe Dawuda ba.”
7 Jonathan appela David, et il lui fit voir toutes ces choses. Puis Jonathan amena David à Saül, et il fut en sa présence comme auparavant.
Ta haka Yonatan ya kira Dawuda ya gaya masa dukan maganarsu. Ya kawo shi wurin Shawulu, Dawuda kuwa ya zauna tare da Shawulu kamar dā.
8 Il y eut de nouveau une guerre. David sortit, combattit les Philistins, et les tua par une grande défaite; ils s'enfuirent devant lui.
Wani yaƙi ya sāke tashi, Dawuda kuwa ya fita ya yaƙi Filistiyawa, ya kai musu hari mai tsanani, sai da suka gudu a gabansa.
9 Un mauvais esprit de Yahvé était sur Saül, qui était assis dans sa maison, sa lance à la main, et David jouait de la musique avec sa main.
Amma mugun ruhu daga Ubangiji ya sauko wa Shawulu yayinda yana zaune a cikin gidansa da māshi a hannunsa. Yayinda Dawuda yake bugan molo,
10 Saül chercha à clouer David au mur avec la lance, mais celui-ci se déroba à la présence de Saül, et il planta la lance dans le mur. David prit la fuite et s'échappa cette nuit-là.
Shawulu ya yi ƙoƙari yă kafe shi da bango da māshinsa, amma Dawuda ya goce sa’ad da Shawulu jefa māshin a bango. A daren nan Dawuda ya nemi hanya ya gudu.
11 Saül envoya des messagers à la maison de David pour le surveiller et le tuer au matin. Mical, la femme de David, lui dit: « Si tu ne sauves pas ta vie cette nuit, demain tu seras tué. »
Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
12 Alors Mical fit descendre David par la fenêtre. Il s'en alla, prit la fuite et s'échappa.
Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
13 Michal prit le théraphim et le coucha dans le lit; elle mit à sa tête un coussin de poils de chèvre et le couvrit de vêtements.
Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
14 Lorsque Saül envoya des messagers pour prendre David, elle dit: « Il est malade. »
Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
15 Saül envoya les messagers voir David, en disant: « Amenez-le-moi sur le lit, afin que je le tue. »
Sai Shawulu ya sāke aiki mutanen su ga Dawuda, ya ce musu, “Ku kawo shi a gādonsa domin in kashe shi.”
16 Lorsque les messagers entrèrent, voici, le théraphim était dans le lit, avec le coussin de poils de chèvre à sa tête.
Amma da mutanen suka shiga sai suka ga gunkin a gadon, a wajen kan kuwa akwai gashin akuya.
17 Saül dit à Mical: « Pourquoi m'as-tu trompé de la sorte et as-tu laissé partir mon ennemi, qui s'est échappé? » Michal répondit à Saül: « Il m'a dit: « Laisse-moi partir! Pourquoi devrais-je te tuer? »
Shawulu ya ce wa Mikal, “Don me kika ruɗe ni har kika bar maƙiyina ya gudu ya tsere?” Mikal ta ce masa, “Ya ce mini, ‘Idan ban bar shi ya tafi ba, zai kashe ni?’”
18 David s'enfuit et s'échappa; il alla trouver Samuel à Rama, et lui raconta tout ce que Saül lui avait fait. Il partit avec Samuel et s'installa à Naïoth.
Da Dawuda ya gudu ya tsere, sai ya tafi wurin Sama’ila a Rama ya gaya masa dukan abin da Shawulu ya yi masa. Da shi da Sama’ila suka tafi Nayiwot suka zauna a can.
19 On fit dire à Saül: « Voici, David est à Naïoth, à Rama. »
Shawulu ya sami labari cewa, “Dawuda yana Nayiwot a Rama.”
20 Saül envoya des messagers pour s'emparer de David; et lorsqu'ils virent la troupe des prophètes en train de prophétiser, et Samuel debout à leur tête, l'Esprit de Dieu vint sur les messagers de Saül, et ils prophétisèrent aussi.
Sai ya aiki mutane su je su kamo Dawuda, amma da suka ga ƙungiyar annabawa suna annabci tare da Sama’ila shugabansu a tsaye, sai Ruhun Allah ya sauko wa mutanen Shawulu, su ma suka fara yin annabci.
21 Lorsque Saül en fut informé, il envoya d'autres messagers, qui prophétisèrent eux aussi. Saül envoya de nouveau des messagers la troisième fois, et ils prophétisèrent aussi.
Shawulu ya sami labari game da wannan, sai ya sāke aiken waɗansu da yawa. Su ma suka shiga yin annabci. Shawulu ya sāke aiken mutane sau na uku, su kuma suka shiga yin annabci.
22 Il alla aussi à Rama, et arriva au grand puits qui est à Secu; il demanda: « Où sont Samuel et David? » L'un d'eux a dit: « Voici, ils sont à Naioth, à Rama. »
A ƙarshe, shi da kansa ya tashi ya tafi Rama. Ya bi ta babban rijiyar ruwan Seku. A can ya yi tambaya ya ce, “Ina Sama’ila da Dawuda suke?” Suka ce, “Suna cikin Nayiwot a Rama.”
23 Il alla ensuite à Naïoth, à Rama. L'Esprit de Dieu vint aussi sur lui, et il continua à prophétiser, jusqu'à ce qu'il arrivât à Naïoth, à Rama.
Saboda haka Shawulu ya tafi Nayiwot a Rama, amma Ruhun Allah ya sauko masa, shi ma ya yi tafiya yana annabci har sai da ya isa Nayiwot.
24 Il se dépouilla aussi de ses vêtements. Il prophétisa aussi devant Samuel et se coucha nu tout ce jour-là et toute cette nuit-là. C'est pourquoi on dit: « Saul est-il aussi au nombre des prophètes? »
Ya tuttuɓe rigunarsa, ya kuma yi annabci a gaban Sama’ila. Ya kwanta tsirara dukan yini da dukan dare. Abin da ya sa ke nan mutane suke cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”

< 1 Samuel 19 >