< 1 Samuel 14 >
1 Un jour, Jonathan, fils de Saül, dit au jeune homme qui portait son armure: « Viens! Allons vers la garnison des Philistins qui est de l'autre côté. » Mais il ne le dit pas à son père.
Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
2 Saül resta à l'extrémité de Guibea, sous le grenadier qui est à Migron, et le peuple qui était avec lui était d'environ six cents hommes,
Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
3 dont Achija, fils d'Achitub, frère d'Ichabod, fils de Phinées, fils d'Eli, prêtre de Yahvé à Silo, portant un éphod. Le peuple ne savait pas que Jonathan était parti.
A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
4 Entre les cols par lesquels Jonathan cherchait à passer à la garnison des Philistins, il y avait un rocher d'un côté et un rocher de l'autre côté; le nom de l'un était Bozez, et le nom de l'autre Seneh.
A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
5 L'un des rochers s'élevait au nord, en face de Michmash, et l'autre au sud, en face de Guéba.
Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
6 Jonathan dit au jeune homme qui portait son armure: « Viens! Allons voir la garnison de ces incirconcis. Il se peut que Yahvé travaille pour nous, car rien n'empêche Yahvé de sauver par beaucoup ou par peu. »
Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
7 Le porteur de l'armure lui dit: « Fais tout ce que tu as dans le cœur. Va, et voici, je suis avec toi selon ton cœur. »
Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
8 Jonathan dit alors: « Voici, nous allons passer devant les hommes et nous nous montrerons à eux.
Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
9 S'ils nous disent: « Attendez que nous venions à vous », nous resterons à notre place et nous ne monterons pas vers eux.
In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
10 Mais s'ils nous disent: « Montez vers nous », nous monterons, car l'Éternel les a livrés entre nos mains. Ce sera pour nous un signe. »
Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
11 Tous deux se révélèrent à la garnison des Philistins, et les Philistins dirent: « Voici les Hébreux qui sortent des trous où ils s'étaient cachés! »
Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
12 Les hommes de la garnison répondirent à Jonathan et à son porteur d'armure en disant: « Venez vers nous, nous allons vous montrer quelque chose! ». Jonathan dit à son porteur d'armes: « Monte après moi, car l'Éternel les a livrés entre les mains d'Israël. »
Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
13 Jonathan monta sur ses mains et sur ses pieds, et le porteur de ses armes le suivit; ils tombèrent devant Jonathan, et le porteur de ses armes les tua après lui.
Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
14 Cette première tuerie, que Jonathan et le porteur de ses armes firent, concernait environ vingt hommes, soit la moitié de la longueur d'un sillon dans un acre de terre.
A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
15 Il y eut un tremblement dans le camp, dans les champs et parmi tout le peuple; la garnison et les pillards tremblèrent aussi; la terre trembla, et il y eut un très grand tremblement.
Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
16 Les sentinelles de Saül, à Guibea de Benjamin, regardèrent; et voici que la foule se fondit et se dispersa.
Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
17 Alors Saül dit au peuple qui était avec lui: « Comptez maintenant, et voyez qui manque parmi nous. » Quand ils eurent compté, voici que Jonathan et le porteur de son armure n'étaient pas là.
Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
18 Saül dit à Achija: « Amène ici l'arche de Dieu. » Car l'arche de Dieu était en ce temps-là avec les enfants d'Israël.
Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
19 Pendant que Saül parlait au prêtre, le tumulte qui régnait dans le camp des Philistins continuait et augmentait; Saül dit au prêtre: « Retire ta main! »
Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
20 Saül et tout le peuple qui était avec lui se rassemblèrent et vinrent au combat; et voici, ils se frappaient tous avec leurs épées dans une très grande confusion.
Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
21 Les Hébreux qui étaient auparavant avec les Philistins et qui étaient montés avec eux dans le camp de tous les côtés, se tournèrent aussi vers les Israélites qui étaient avec Saül et Jonathan.
Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
22 De même, tous les hommes d'Israël qui s'étaient cachés dans la montagne d'Ephraïm, ayant appris la fuite des Philistins, les suivirent de près dans la bataille.
Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
23 L'Éternel sauva Israël ce jour-là, et la bataille passa près de Beth Aven.
Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
24 Ce jour-là, les hommes d'Israël furent dans l'angoisse, car Saül avait adressé au peuple cette injonction: « Maudit soit l'homme qui mangera quelque chose jusqu'au soir, et je serai vengé de mes ennemis. » Ainsi, aucun des membres du peuple ne goûta de nourriture.
A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
25 Tout le peuple entra dans la forêt; et il y avait du miel sur le sol.
Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
26 Quand le peuple fut arrivé dans la forêt, voici que du miel coulait, mais personne ne mit la main à sa bouche, car le peuple craignait le serment.
Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
27 Mais Jonathan n'entendit pas quand son père donna l'ordre au peuple de prêter serment. Il sortit donc l'extrémité de la verge qu'il tenait à la main, la trempa dans le rayon de miel et porta la main à sa bouche; et ses yeux s'illuminèrent.
Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
28 Alors l'un des membres du peuple prit la parole et dit: « Ton père a donné un ordre direct au peuple, avec serment, en disant: « Maudit soit l'homme qui mange aujourd'hui. » Alors, le peuple s'évanouit.
Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
29 Jonathan dit alors: « Mon père a troublé le pays. Voyez comme mes yeux se sont éclaircis parce que j'ai goûté un peu de ce miel.
Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
30 Combien plus, si le peuple avait mangé aujourd'hui du butin de ses ennemis qu'il a trouvé? Car il n'y a pas eu de grand carnage chez les Philistins. »
Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
31 Ce jour-là, ils frappèrent les Philistins depuis Michmash jusqu'à Ajalon. Le peuple était très affaibli.
A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
32 Le peuple se jeta sur le butin, prit des moutons, des bœufs et des veaux, les tua à terre, et le peuple les mangea avec le sang.
Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
33 On en informa Saül, en disant: « Voici que le peuple pèche contre l'Éternel, en mangeant de la viande avec le sang. » Il a dit: « Tu as été déloyal. Fais-moi rouler une grosse pierre aujourd'hui! »
Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
34 Saül dit: « Dispersez-vous parmi le peuple, et dites-leur: « Que chacun m'amène ici son bœuf et que chacun amène son mouton, que vous les tuiez ici, et que vous mangiez; et ne péchez pas contre Yahvé en mangeant de la viande avec le sang. » Tout le peuple amena chacun son bœuf cette nuit-là, et les tua là.
Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
35 Saül bâtit un autel à Yahvé. Ce fut le premier autel qu'il construisit à l'Éternel.
Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
36 Saül dit: « Descendons après les Philistins pendant la nuit, et faisons du pillage parmi eux jusqu'à la lumière du matin. Ne laissons pas un seul homme parmi eux. » Ils ont dit: « Fais ce qui te semble bon. » Alors le prêtre a dit: « Approchons-nous ici de Dieu. »
Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
37 Saül demanda conseil à Dieu: « Dois-je descendre après les Philistins? Les livreras-tu entre les mains d'Israël? » Mais il ne lui répondit pas ce jour-là.
Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
38 Saül dit: « Approchez ici, vous tous, chefs du peuple, et sachez et voyez en qui ce péché a été commis aujourd'hui.
Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
39 Car l'Éternel est vivant, lui qui sauve Israël, et si c'est en Jonathan, mon fils, qu'il a péché, il mourra. » Mais il n'y eut pas un homme parmi tout le peuple qui lui répondit.
Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
40 Alors il dit à tout Israël: « Vous serez d'un côté, et moi et Jonathan, mon fils, nous serons de l'autre côté. » Le peuple dit à Saul: « Fais ce qui te semble bon. »
Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
41 Saül dit à Yahvé, le Dieu d'Israël: « Montre la droite. » Jonathan et Saul ont été choisis, mais le peuple s'est échappé.
Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
42 Saül dit: « Jetez le sort entre moi et Jonathan, mon fils. » Jonathan a été sélectionné.
Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
43 Alors Saül dit à Jonathan: « Dis-moi ce que tu as fait! » Jonathan lui en fit part et dit: « J'ai certainement goûté un peu de miel avec le bout de la verge qui était dans ma main; et voici que je dois mourir. »
Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
44 Saül dit: « Que Dieu fasse ainsi et plus encore, car tu vas mourir, Jonathan. »
Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
45 Le peuple dit à Saül: « Jonathan va-t-il mourir, lui qui a opéré ce grand salut en Israël? Loin de là! Yahvé est vivant, il ne tombera pas à terre un seul cheveu de sa tête, car il a travaillé avec Dieu aujourd'hui! ». Le peuple sauva donc Jonathan, et il ne mourut pas.
Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
46 Puis Saül cessa de suivre les Philistins, et les Philistins s'en allèrent chez eux.
Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
47 Lorsque Saül eut pris le pouvoir sur Israël, il combattit tous ses ennemis de toutes parts: contre Moab, contre les enfants d'Ammon, contre Édom, contre les rois de Tsoba et contre les Philistins. Partout où il se tournait, il les battait.
Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
48 Il fit preuve de vaillance, frappa les Amalécites et délivra Israël des mains de ceux qui le pillaient.
Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
49 Les fils de Saül étaient Jonathan, Ishvi et Malkishua; et les noms de ses deux filles étaient les suivants: le nom de l'aînée Merab, et le nom de la cadette Mical.
’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
50 Le nom de la femme de Saül était Ahinoam, fille d'Ahimaaz. Le nom du chef de son armée était Abner, fils de Ner, oncle de Saül.
Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
51 Kish était le père de Saül, et Ner, père d'Abner, était le fils d'Abiel.
Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
52 Il y eut une guerre sévère contre les Philistins pendant toute la durée de Saül; et quand Saül voyait un homme fort ou un homme vaillant, il le prenait à son service.
Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.