< 1 Samuel 13 >

1 Saül avait trente ans lorsqu'il devint roi, et il régna sur Israël pendant quarante-deux ans.
Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
2 Saül choisit pour lui trois mille hommes d'Israël, dont deux mille étaient avec Saül à Micmasch et sur la montagne de Béthel, et mille étaient avec Jonathan à Guibea de Benjamin. Il envoya le reste du peuple dans ses tentes.
Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
3 Jonathan frappa la garnison des Philistins qui était à Guéba, et les Philistins l'apprirent. Saül fit sonner la trompette dans tout le pays, en disant: « Que les Hébreux entendent! »
Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
4 Tout Israël apprit que Saül avait frappé la garnison des Philistins, et aussi qu'Israël était considéré comme une abomination par les Philistins. Le peuple se rassembla après Saül à Guilgal.
Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
5 Les Philistins se rassemblèrent pour combattre Israël: trente mille chars, six mille cavaliers, et un peuple nombreux comme le sable qui est au bord de la mer. Ils montèrent et campèrent à Micmasch, à l'orient de Beth Aven.
Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
6 Lorsque les hommes d'Israël virent qu'ils étaient en difficulté (car le peuple était en détresse), alors le peuple se cacha dans des cavernes, dans des fourrés, dans des rochers, dans des tombeaux et dans des fosses.
Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
7 Une partie des Hébreux avait traversé le Jourdain pour se rendre au pays de Gad et de Galaad; quant à Saül, il était encore à Guilgal, et tout le peuple le suivait en tremblant.
Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
8 Il resta sept jours, selon le temps fixé par Samuel; mais Samuel n'était pas venu à Guilgal, et le peuple se dispersait devant lui.
Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
9 Saül dit: « Apportez-moi ici l'holocauste et les sacrifices de paix. » Il offrit l'holocauste.
Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
10 Dès qu'il eut achevé d'offrir l'holocauste, voici que Samuel arriva; Saül sortit à sa rencontre pour le saluer.
Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
11 Samuel dit: « Qu'as-tu fait? » Saül dit: « Parce que j'ai vu que le peuple s'était dispersé loin de moi, que tu n'étais pas venu dans les jours fixés, et que les Philistins s'étaient rassemblés à Michmash,
Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
12 j'ai donc dit: « Maintenant les Philistins vont descendre sur moi jusqu'à Gilgal, et je n'ai pas imploré la faveur de Yahvé. Je me suis donc forcé et j'ai offert l'holocauste. »
sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
13 Samuel dit à Saül: « Tu as fait une folie. Tu n'as pas observé le commandement de l'Éternel, ton Dieu, qu'il t'avait donné; car maintenant l'Éternel aurait établi ton règne sur Israël pour toujours.
Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
14 Mais maintenant, ton règne ne durera pas. L'Éternel s'est cherché un homme selon son cœur, et l'Éternel l'a établi prince sur son peuple, parce que vous n'avez pas gardé ce que l'Éternel vous avait commandé. »
Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
15 Samuel se leva et alla de Guilgal à Guibea de Benjamin. Saül compta le peuple qui était présent avec lui, soit environ six cents hommes.
Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
16 Saül, Jonathan, son fils, et le peuple qui était avec eux, restèrent à Guéba de Benjamin; mais les Philistins campaient à Micmash.
Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
17 Les pillards sortirent du camp des Philistins en trois compagnies: une compagnie prit le chemin qui mène à Ophra, au pays de Shual;
Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
18 une autre compagnie prit le chemin de Beth Horon; et une autre compagnie prit le chemin de la frontière qui regarde la vallée de Zeboïm vers le désert.
Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
19 Il n'y avait pas de forgeron dans tout le pays d'Israël, car les Philistins avaient dit: « De peur que les Hébreux ne se fabriquent des épées ou des lances ».
Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
20 Mais tous les Israélites descendirent chez les Philistins, chacun aiguisant son soc, sa hache et sa faucille.
Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
21 Le prix était d'un payim par personne pour aiguiser les socs, les socs de charrue, les fourches, les haches et les aiguillons.
Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
22 Au jour du combat, on ne trouva ni épée ni lance dans la main d'aucun des gens qui étaient avec Saül et Jonathan, mais Saül et Jonathan, son fils, les avaient.
A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
23 La garnison des Philistins sortit au col de Micmash.
Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.

< 1 Samuel 13 >