< 1 Samuel 12 >
1 Samuel dit à tout Israël: « Voici, j'ai écouté votre voix dans tout ce que vous m'avez dit, et j'ai établi un roi sur vous.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 Maintenant, voici que le roi marche devant vous. Je suis vieux et j'ai les cheveux blancs. Voici, mes fils sont avec toi. J'ai marché devant toi depuis ma jeunesse jusqu'à ce jour.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 Me voici. Témoigne contre moi devant Yahvé et devant son oint. De qui ai-je pris le bœuf? A qui appartient l'âne que j'ai pris? Qui ai-je spolié? Qui ai-je opprimé? De la main de qui ai-je pris un pot-de-vin pour me faire aveugler les yeux? Je vous le rendrai. »
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 Ils dirent: « Tu ne nous as pas escroqués, tu ne nous as pas opprimés, et tu n'as rien pris de la main de personne. »
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 Il leur dit: « Yahvé est témoin contre vous, et son oint est témoin aujourd'hui, que vous n'avez rien trouvé dans ma main. » Ils répondirent: « Il est témoin. »
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Samuel dit au peuple: « C'est Yahvé qui a établi Moïse et Aaron, et qui a fait monter vos pères du pays d'Égypte.
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Maintenant, restez immobiles, afin que je puisse plaider avec vous devant Yahvé au sujet de toutes les actions justes de Yahvé, qu'il a accomplies envers vous et envers vos pères.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 « Lorsque Jacob entra en Égypte et que vos pères crièrent à Yahvé, Yahvé envoya Moïse et Aaron, qui firent sortir vos pères d'Égypte et les firent habiter dans ce lieu.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 Mais ils oublièrent Yahvé, leur Dieu, qui les vendit entre les mains de Sisera, chef de l'armée de Hatsor, entre les mains des Philistins et entre les mains du roi de Moab, et qui les combattit.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 Ils crièrent à Yahvé et dirent: « Nous avons péché, car nous avons abandonné Yahvé et nous avons servi les Baals et les Ashtaroths; maintenant, délivre-nous de la main de nos ennemis et nous te servirons ».
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 Yahvé a envoyé Jerubbaal, Bedan, Jephté et Samuel, et il vous a délivrés de la main de vos ennemis de tous bords, et vous avez vécu en sécurité.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 « Quand tu as vu que Nahash, roi des enfants d'Ammon, est venu contre toi, tu m'as dit: « Non, mais un roi régnera sur nous », alors que Yahvé ton Dieu était ton roi.
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 Maintenant, voyez le roi que vous avez choisi et que vous avez demandé. Voici que l'Éternel a établi un roi sur vous.
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 Si tu crains l'Éternel, si tu le sers, si tu écoutes sa voix et si tu ne te révoltes pas contre le commandement de l'Éternel, alors toi et le roi qui règne sur toi, vous êtes disciples de l'Éternel, votre Dieu.
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 Mais si vous n'écoutez pas la voix de l'Éternel et si vous vous rebellez contre le commandement de l'Éternel, la main de l'Éternel sera contre vous, comme elle a été contre vos pères.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 Maintenant, restez immobiles et regardez cette grande chose que Yahvé va faire sous vos yeux.
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 N'est-ce pas aujourd'hui la moisson du blé? J'appellerai Yahvé, pour qu'il envoie le tonnerre et la pluie; et vous saurez et verrez que votre méchanceté est grande, celle que vous avez commise aux yeux de Yahvé, en demandant un roi. »
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Samuel invoqua Yahvé, et Yahvé envoya le tonnerre et la pluie ce jour-là. Et tout le peuple eut une grande crainte de Yahvé et de Samuel.
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 Tout le peuple dit à Samuel: « Prie pour tes serviteurs l'Éternel, ton Dieu, afin que nous ne mourions pas; car nous avons ajouté à tous nos péchés cette faute, celle de demander un roi. »
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 Samuel dit au peuple: « N'ayez pas peur. Vous avez fait tout ce mal, mais ne vous détournez pas de Yahvé, et servez Yahvé de tout votre cœur.
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 Ne vous détournez pas pour aller après des choses vaines qui ne peuvent ni profiter ni délivrer, car elles sont vaines.
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 Car l'Éternel n'abandonnera pas son peuple à cause de son grand nom, car il a plu à l'Éternel de faire de vous un peuple pour lui.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 Quant à moi, loin de moi l'idée de pécher contre l'Éternel en cessant de prier pour vous, mais je vous instruirai dans la bonne et juste voie.
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 Craignez Yahvé et servez-le fidèlement de tout votre cœur, car considérez les grandes choses qu'il a faites pour vous.
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 Mais si vous persistez à faire le mal, vous périrez, vous et votre roi. »
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.