< 1 Rois 9 >

1 Lorsque Salomon eut achevé de bâtir la maison de Yahvé, la maison du roi, et tout ce qu'il lui plut de faire,
Sa’ad da Solomon ya gama ginin haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki, ya kuma yi dukan abin da yake so yă yi,
2 Yahvé apparut à Salomon pour la seconde fois, comme il lui était apparu à Gabaon.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi sau na biyu, kamar yadda ya bayyana masa a Gibeyon.
3 Yahvé lui dit: « J'ai entendu ta prière et ta supplication que tu as présentées devant moi. J'ai sanctifié cette maison que tu as bâtie, pour y mettre mon nom à jamais, et mes yeux et mon cœur y seront toujours.
Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu’arka da kuma roƙon da ka yi a gabana; na tsarkake wannan haikali wanda ka gina, ta wurinsa Sunana zai kasance a can har abada. Idanuna da zuciyata kullum za su kasance a can.
4 Si tu marches devant moi comme a marché David, ton père, dans l'intégrité de ton cœur et dans la droiture, pour faire tout ce que je t'ai commandé, et si tu observes mes lois et mes ordonnances,
“Kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana da mutunci a zuci da kuma gaskiya, kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka yi dukan abin da na umarta, ka kuma yi biyayya da ƙa’idodina da kuma dokokina,
5 j'affermirai pour toujours le trône de ton royaume sur Israël, comme je l'ai promis à David, ton père, en disant: « Il ne manquera pas de toi un homme sur le trône d'Israël ».
zan kafa kujerar sarautarka a bisa Isra’ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani a kan kujerar sarautar Isra’ila ba.’
6 Mais si vous vous détournez de moi, vous ou vos enfants, et si vous n'observez pas mes commandements et mes lois que j'ai mis devant vous, mais si vous allez servir d'autres dieux et vous prosterner devant eux,
“Amma in kai, ko’ya’yanka maza, suka juye daga gare ni, ba ku kuma kiyaye umarnai da ƙa’idodin da na ba ku ba, kuka yi gaba, kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka kuma yi musu sujada,
7 alors je retrancherai Israël du pays que je lui ai donné, et je rejetterai loin de moi cette maison que j'ai sanctifiée pour mon nom, et Israël sera un sujet de sarcasme et de moquerie parmi tous les peuples.
sai in yanke mutanen Isra’ila daga ƙasar da na ba su, in kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Isra’ila kuwa za tă zama abin gori da abin dariya a cikin dukan mutane.
8 Malgré la hauteur de cette maison, tous ceux qui passeront près d'elle seront étonnés et siffleront, et ils diront: « Pourquoi Yahvé a-t-il fait cela à ce pays et à cette maison? »
Wannan haikali zai zama tarin juji. Duk wanda ya wuce ta hanyan nan kuwa zai ji tausayi, yă kuma yi tsaki yana cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka ga wannan ƙasa da kuma wannan haikali?’
9 Et ils répondront: « Parce qu'ils ont abandonné Yahvé, leur Dieu, qui a fait sortir leurs pères du pays d'Égypte, et qu'ils ont embrassé d'autres dieux, se sont prosternés devant eux et les ont servis. C'est pourquoi Yahvé a fait venir sur eux tout ce malheur. »
Mutane za su amsa su ce, ‘Saboda sun yashe Ubangiji Allahnsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna yin musu sujada, suna bauta musu ne, ya sa Ubangiji ya kawo dukan masifan nan a kansu.’”
10 Au bout de vingt ans, pendant lesquels Salomon avait construit les deux maisons, la maison de Yahvé et la maison du roi
A ƙarshen shekaru ashirin da Solomon ya ɗauka yana gina haikalin Ubangiji da fadan sarki,
11 (Hiram, roi de Tyr, avait fourni à Salomon des cèdres et des cyprès, et de l'or, selon tout son désir), le roi Salomon donna à Hiram vingt villes au pays de Galilée.
sai Sarki Solomon ya ba wa Hiram sarkin Taya garuruwa ashirin a yankin Galili, gama Hiram ya tanada masa da dukan katakai al’ul da na fir, da kuma zinariyar da ya bukaci domin aiki.
12 Hiram sortit de Tyr pour voir les villes que Salomon lui avait données, et elles ne lui plurent pas.
Amma sa’ad da Hiram ya zo daga Taya don yă ga garuruwan da Solomon ya ba shi, sai bai ji daɗi ba.
13 Il dit: « Quelles sont ces villes que tu m'as données, mon frère? » Il les appela jusqu'à ce jour le pays de Cabul.
Sai ya ce, “Wanda irin garuruwa ke nan ka ba ni, ɗan’uwana?” Saboda haka ya kira su Ƙasar Kabul, sunan da suke da shi har wa yau.
14 Hiram envoya au roi cent vingt talents d'or.
Hiram kuwa ya aika wa sarki talenti 120 na zinariya.
15 C'est la raison des travaux forcés auxquels le roi Salomon s'est astreint: construire la maison de Yahvé, sa propre maison, Millo, la muraille de Jérusalem, Hazor, Megiddo et Guézer.
Ga lissafin ma’aikatan gandun da Sarki Solomon ya ɗauka don ginin haikalin Ubangiji, da fadarsa, da madogaran gini, da katangar Urushalima, da kuma Hazor Megiddo da Gezer.
16 Pharaon, roi d'Égypte, était monté, s'était emparé de Guézer, l'avait incendiée, avait tué les Cananéens qui habitaient la ville et l'avait donnée en cadeau de mariage à sa fille, la femme de Salomon.
(Fir’auna sarkin Masar ya kai wa Gezer hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Ya sa mata wuta, ya kashe Kan’aniyawanta mazaunan wurin, ya kuma ba da ita a matsayin kyautar aure ga’yarsa, matar Solomon.
17 Salomon bâtit dans le pays Guézer, Beth Horon la basse,
Solomon kuwa ya sāke gina Gezer.) Ya gina Bet-Horon ta Kwari,
18 Baalath, Tamar dans le désert,
da Ba’alat, da Tadmor a hamada, na cikin ƙasarsa.
19 toutes les villes de stockage que possédait Salomon, les villes pour ses chars, les villes pour ses cavaliers, et ce que Salomon voulait bâtir pour son plaisir à Jérusalem, au Liban et dans tout le pays de sa domination.
Haka kuma ya gina dukan biranen ajiyarsa, da garuruwa domin kekunan yaƙinsa, da garuruwa domin dawakansa. Ya gina duk abin da ya so yă ginawa a Urushalima, da Lebanon, da kuma ko’ina a dukan yankin da ya yi mulki.
20 Quant à tout le peuple qui restait des Amoréens, des Héthiens, des Phéréziens, des Héviens et des Jébusiens, et qui n'appartenait pas aux enfants d'Israël,
Dukan Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa da Yebusiyawan da suka ragu a ƙasar (waɗanda ba Isra’ilawa ba ne),
21 leurs enfants restés après eux dans le pays, et que les enfants d'Israël n'ont pas pu détruire par interdit, Salomon a levé un tribut de serviteurs jusqu'à ce jour.
wato, waɗanda suka ragu a ƙasar, waɗanda Isra’ilawa ba su iya hallakawa ba, su ne Solomon ya ɗauka su zama bayinsa don aikin gandu, kamar yadda yake har wa yau.
22 Mais Salomon n'établit pas de serviteurs parmi les enfants d'Israël; ce furent les hommes de guerre, ses serviteurs, ses chefs, ses capitaines, les chefs de ses chars et de ses cavaliers.
Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi ba; su ne mayaƙansa, shugabannin gwamnatinsa, dogarawansa, shugabannin sojojinsa, da shugabanninsa na kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙinsa.
23 Tels étaient les cinq cent cinquante chefs qui dirigeaient l'œuvre de Salomon, et qui avaient autorité sur le peuple qui travaillait à l'œuvre.
Su ne kuma manyan shugabanni masu lura da ayyukan Solomon, su ne shugabanni 550 masu lura da mutanen da suke aiki.
24 Mais la fille de Pharaon monta de la cité de David dans sa maison que Salomon avait construite pour elle. Puis il construisit Millo.
Bayan’yar Fir’auna ta haura daga Birnin Dawuda zuwa fadan da Solomon ya gina mata, sai ya gina madogaran gini.
25 Salomon offrait des holocaustes et des sacrifices de prospérité sur l'autel qu'il construisait pour Yahvé, trois fois par an, et il brûlait des parfums sur l'autel qui était devant Yahvé. Il acheva donc la maison.
Sau uku a shekara Solomon kan miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji, yana ƙone turare a gaban Ubangiji haɗe da su, ta haka ya cika abin da ake bukata na haikali.
26 Le roi Salomon fit construire une flotte de navires à Ezion Geber, qui est près d'Eloth, sur les bords de la mer Rouge, dans le pays d'Édom.
Sarki Solomon ya kuma gina jiragen ruwa a Eziyon Geber, wadda take kusa da Elot a Edom, a bakin Jan Teku.
27 Hiram envoya dans la flotte ses serviteurs, des marins qui connaissaient la mer, avec les serviteurs de Salomon.
Hiram kuwa ya aiki mutanensa, masu tuƙan jirgin ruwa waɗanda suka san teku, don su yi hidima a jerin jiragen ruwa tare da mutanen Solomon.
28 Ils arrivèrent à Ophir, y prirent de l'or, quatre cent vingt talents, et l'apportèrent au roi Salomon.
Suka tafi Ofir suka kuma dawo da talenti 420 na zinariya, wanda suka ba wa Sarki Solomon.

< 1 Rois 9 >