< 1 Rois 20 >

1 Ben Hadad, roi de Syrie, rassembla toute son armée, et il y avait avec lui trente-deux rois, avec des chevaux et des chars. Il monta et assiégea Samarie, et il la combattit.
Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
2 Il envoya des messagers dans la ville à Achab, roi d'Israël, et lui dit: « Ben Hadad dit:
Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
3 Ton argent et ton or sont à moi. Tes femmes aussi et tes enfants, même les meilleurs, sont à moi. »
‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
4 Le roi d'Israël répondit: « C'est ce que tu as dit, mon seigneur, ô roi. Je suis à toi, avec tout ce que j'ai. »
Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
5 Les messagers revinrent et dirent: « Ben Hadad dit: « Je t'ai effectivement envoyé dire: « Tu me livreras ton argent, ton or, tes femmes et tes enfants;
Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
6 mais je t'enverrai mes serviteurs demain à cette heure-ci, et ils fouilleront ta maison et les maisons de tes serviteurs. Tout ce qui sera agréable à vos yeux, ils le mettront dans leur main et l'emporteront. »'"
Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
7 Alors le roi d'Israël appela tous les anciens du pays et dit: « Remarquez, je vous prie, comment cet homme cherche le malheur, car il m'a envoyé chercher mes femmes et mes enfants, mon argent et mon or, et je ne l'ai pas refusé. »
Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
8 Tous les anciens et tout le peuple lui dirent: « N'écoute pas, et ne consens pas. »
Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
9 Il dit donc aux messagers de Ben Hadad: « Dis à mon seigneur le roi: « Je ferai tout ce que tu as envoyé à ton serviteur au début, mais je ne peux pas faire ceci. » Les messagers partirent et lui rapportèrent le message.
Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
10 Ben Hadad lui envoya un message et dit: « Les dieux me font ainsi, et plus encore, si la poussière de Samarie suffit en poignées pour tout le peuple qui me suit. »
Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
11 Le roi d'Israël répondit: « Dis-lui: 'Que celui qui met son armure ne se vante pas comme celui qui l'enlève'. »
Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
12 Lorsque Ben Hadad entendit ce message alors qu'il buvait, lui et les rois dans les pavillons, il dit à ses serviteurs: « Préparez-vous à attaquer! » Ils se préparèrent donc à attaquer la ville.
Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
13 Voici qu'un prophète s'approcha d'Achab, roi d'Israël, et dit: « L'Éternel dit: As-tu vu toute cette grande foule? Voici que je vais la livrer aujourd'hui entre tes mains. Alors tu sauras que je suis Yahvé. »
Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
14 Achab a dit: « Par qui? » Il dit: « Yahvé dit: 'Par les jeunes gens des princes des provinces'. » Puis il a dit: « Qui va commencer la bataille? » Il a répondu: « Vous. »
Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
15 Il rassembla ensuite les jeunes gens des chefs des provinces, au nombre de deux cent trente-deux. Après eux, il rassembla tout le peuple, tous les enfants d'Israël, au nombre de sept mille.
Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
16 Ils sortirent à midi. Mais Ben Hadad s'enivrait dans les pavillons, lui et les rois, les trente-deux rois qui l'avaient aidé.
Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
17 Les jeunes gens des princes des provinces sortirent les premiers; Ben Hadad les fit sortir, et on lui dit: « Des hommes sortent de Samarie. »
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
18 Il dit: « S'ils sont sortis pour la paix, prenez-les vivants; ou s'ils sont sortis pour la guerre, prenez-les vivants. »
Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
19 Ils sortirent donc de la ville, les jeunes gens des chefs de province et l'armée qui les suivait.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
20 Ils tuèrent chacun leur homme. Les Syriens prirent la fuite, et Israël les poursuivit. Ben Hadad, roi de Syrie, s'échappa sur un cheval avec des cavaliers.
Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
21 Le roi d'Israël sortit, frappa les chevaux et les chars, et tua les Syriens par une grande défaite.
Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
22 Le prophète s'approcha du roi d'Israël et lui dit: « Va, fortifie-toi et prévois ce que tu dois faire, car au retour de l'année, le roi de Syrie montera contre toi. »
Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
23 Les serviteurs du roi de Syrie lui dirent: « Leur dieu est un dieu des collines; c'est pourquoi ils ont été plus forts que nous. Mais combattons-les dans la plaine, et nous serons sûrement plus forts qu'eux.
Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
24 Fais ceci: enlève les rois, chacun à sa place, et mets des chefs à leur place.
Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
25 Rassemblez une armée comme celle que vous avez perdue, cheval contre cheval et char contre char. Nous les affronterons dans la plaine, et nous serons plus forts qu'eux. » Il écouta leur voix et fit ainsi.
Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
26 Au retour de l'année, Ben Hadad rassembla les Syriens et monta à Aphek pour combattre Israël.
Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
27 Les enfants d'Israël furent rassemblés et reçurent des provisions, puis ils marchèrent contre eux. Les enfants d'Israël campèrent devant eux comme deux petits troupeaux de chevreaux, mais les Syriens remplirent le pays.
Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
28 Un homme de Dieu s'approcha et parla au roi d'Israël, en disant: « L'Éternel dit: Parce que les Syriens ont dit: « L'Éternel est le dieu des collines, mais il n'est pas le dieu des vallées », je livrerai entre tes mains toute cette grande multitude, et tu sauras que je suis l'Éternel. »
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
29 Ils campèrent l'un en face de l'autre pendant sept jours. Le septième jour, le combat fut engagé, et les enfants d'Israël tuèrent en un jour cent mille hommes de pied des Syriens.
Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
30 Mais les autres s'enfuirent à Aphek, dans la ville, et la muraille tomba sur les vingt-sept mille hommes qui restaient. Ben Hadad s'enfuit et entra dans la ville, dans une pièce intérieure.
Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
31 Ses serviteurs lui dirent: « Voici, nous avons appris que les rois de la maison d'Israël sont des rois miséricordieux. S'il te plaît, mettons des sacs sur nos corps et des cordes sur nos têtes, et sortons vers le roi d'Israël. Peut-être te sauvera-t-il la vie. »
Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
32 Ils mirent donc un sac sur leur corps et des cordes sur leur tête, puis ils se présentèrent au roi d'Israël et dirent: « Ton serviteur Ben Hadad dit: « Je t'en prie, laisse-moi vivre. » Il a dit: « Il est encore en vie? C'est mon frère. »
Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
33 Or, les hommes observaient diligemment et se hâtaient de prendre cette phrase; et ils disaient: « Ton frère Ben Hadad. » Puis il a dit: « Va, amène-le. » Ben Hadad sortit vers lui, et le fit monter dans le char.
Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
34 Ben Hadad lui dit: « Je rétablirai les villes que mon père a prises à ton père. Tu te feras des rues à Damas, comme mon père en a fait à Samarie. » « Je », dit Achab, « te laisserai partir avec cette alliance. » Il fit donc une alliance avec lui et le laissa partir.
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
35 Un homme d'entre les fils des prophètes dit à son compagnon par la parole de Yahvé: « Frappe-moi, je te prie! » L'homme refusa de le frapper.
Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
36 Il lui dit alors: « Parce que tu n'as pas obéi à la voix de Yahvé, voici que, dès que tu t'éloigneras de moi, un lion te tuera. » Dès qu'il se fut éloigné de lui, un lion le trouva et le tua.
Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
37 Puis il trouva un autre homme, et dit: « Je te prie de me frapper. » L'homme le frappa et le blessa.
Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
38 Le prophète s'en alla et attendit le roi sur le chemin, et il se déguisa avec son bandeau sur les yeux.
Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
39 Comme le roi passait par là, il cria au roi et lui dit: « Ton serviteur est sorti au milieu de la bataille, et voici qu'un homme est venu m'amener un homme et m'a dit: « Garde cet homme! Si, par hasard, il disparaît, alors ta vie vaudra la sienne, ou bien tu paieras un talent d'argent.'
Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
40 Comme ton serviteur était occupé ici et là, il a disparu. » Le roi d'Israël lui dit: « Il en sera ainsi de ton jugement. C'est toi-même qui l'as décidé. »
Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
41 Il se hâta et ôta le bandeau de ses yeux, et le roi d'Israël reconnut qu'il était l'un des prophètes.
Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
42 Il lui dit: « L'Éternel dit: « Parce que tu as laissé échapper de ta main l'homme que j'avais voué à la destruction, ta vie prendra la place de sa vie, et ton peuple prendra la place de son peuple ». »
Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
43 Le roi d'Israël s'en alla dans sa maison, renfrogné et furieux, et vint à Samarie.
Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.

< 1 Rois 20 >