< 1 Chroniques 29 >

1 Le roi David dit à toute l'assemblée: « Salomon, mon fils, que Dieu seul a choisi, est encore jeune et tendre, et l'ouvrage est grand; car le palais n'est pas pour un homme, mais pour Yahvé Dieu.
Sa’an nan Sarki Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ɗana Solomon, wanda Allah ya zaɓa, matashi ne, kuma bai gogu ba. Aikin yana da yawa, domin wannan ƙasaitaccen ginin ba na mutum ba ne, na Ubangiji Allah ne.
2 J'ai préparé de toutes mes forces, pour la maison de mon Dieu, de l'or pour ce qui est d'or, de l'argent pour ce qui est d'argent, du bronze pour ce qui est de bronze, du fer pour ce qui est de fer, du bois pour ce qui est de bois, des pierres d'onyx, des pierres à enchâsser, des pierres à incruster de diverses couleurs, toutes sortes de pierres précieuses et des pierres de marbre en abondance.
Na riga na tara dukan kayayyakin da na tanada saboda haikalin Allahna, zinariya saboda dukan ayyukan zinariya, azurfa saboda ayyukan azurfa, tagulla saboda ayyukan tagulla, ƙarfe saboda ayyukan ƙarfe da kuma katako saboda ayyukan katako, da onis don ado, turkuwoyis, duwatsu masu launi dabam-dabam, da kuma dukan duwatsu masu kyau da mabul, dukan waɗannan suna nan jingim.
3 De plus, comme j'ai jeté mon dévolu sur la maison de mon Dieu, comme j'ai un trésor personnel d'or et d'argent, je le donne à la maison de mon Dieu, en sus de tout ce que j'ai préparé pour la maison sainte:
Ban da haka ma, cikin sa zuciyata ga haikalin Allahna, yanzu na ba da ma’ajina na zinariya da azurfa saboda haikalin Allahna, fiye da kome na tanada saboda wannan haikali,
4 trois mille talents d'or, de l'or d'Ophir, et sept mille talents d'argent fin, pour revêtir les murs des maisons,
talenti dubu uku na zinariya (zinariyar Ofir) da tacecciyar azurfa dubu bakwai; don adon bangon gine-ginen,
5 d'or pour les objets d'or, d'argent pour les objets d'argent, et pour toutes sortes d'ouvrages à faire par les mains des artisans. Qui donc se propose aujourd'hui de se consacrer volontairement à Yahvé? »
don aikin zinariya da kuma aikin azurfa, don kuma dukan aikin da gwanaye za su yi. Yanzu fa wa yake da niyya yă miƙa kansa a yau don Ubangiji?”
6 Alors les chefs des maisons paternelles, les chefs des tribus d'Israël, les chefs de milliers et de centaines, et les responsables des travaux du roi firent des offrandes volontaires.
Sai shugabannin iyalai, shugabannin kabilan Isra’ila, manyan hafsoshin mayaƙa dubu-dubu da manyan hafsoshi mayaƙa ɗari-ɗari, da shugabannin lura da ayyukan sarki suka yi bayarwa da yardar rai.
7 Ils donnèrent pour le service de la maison de Dieu cinq mille talents d'or et dix mille dariques, dix mille talents d'argent, dix-huit mille talents d'airain et cent mille talents de fer.
Suka bayar talenti dubu biyar na zinariya, talenti dubu goma na azurfa, talenti dubu goma sha takwas na tagulla da talenti dubu ɗari na ƙarfe don aiki a haikalin Allah.
8 Les gens chez qui on trouvait des pierres précieuses les donnèrent au trésor de la maison de l'Éternel, sous la direction de Jehiel, le Gershonite.
Duk waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka ba da su ga Yehiyel mutumin Gershon ma’ajin haikalin Ubangiji.
9 Le peuple se réjouit, parce qu'il avait fait des offrandes volontaires, parce qu'il avait fait des offrandes volontaires à l'Éternel avec un cœur parfait, et le roi David se réjouit aussi avec une grande joie.
Mutane suka yi farin ciki ganin yadda shugabanninsu suke bayarwa da yardar rai, gama sun bayar hannu sake da kuma dukan zuciya ga Ubangiji. Dawuda sarki shi ma ya yi farin ciki ƙwarai.
10 David bénit Yahvé devant toute l'assemblée, et il dit: « Tu es béni, Yahvé, le Dieu d'Israël, notre père, pour les siècles des siècles.
Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, yana cewa, “Yabo gare ka, ya Ubangiji, Allah na mahaifinmu Isra’ila, har abada abadin.
11 A toi, Yahvé, la grandeur, la puissance, la gloire, la victoire et la majesté! Car tout ce qui est dans les cieux et sur la terre t'appartient. C'est à toi qu'appartient le royaume, Yahvé, et tu es élevé comme chef au-dessus de tout.
Girma da iko da ɗaukaka, da daraja da kuma nasara naka ne, ya Ubangiji, gama kome a sama da ƙasa naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji; an kuma ɗaukaka ka a matsayin kai a bisa duka.
12 C'est de toi que viennent la richesse et la gloire, et c'est toi qui domines tout. Dans ta main sont la puissance et la force! C'est dans ta main que se trouve la grandeur et la force de tous!
Wadata da girma daga gare ka suke; kai ne mai mulkin dukan abubuwa. A hannuwanka ne ƙarfi da iko suke don ka ɗaukaka da kuma ba da ƙarfi ga duka.
13 Maintenant, notre Dieu, nous te remercions et nous louons ton nom glorieux.
Yanzu fa, Allahnmu, muna gode maka, muna kuma yabon ɗaukakar sunanka.
14 Mais qui suis-je, et qui est mon peuple, pour que nous puissions faire une telle offrande? Car tout vient de toi, et nous t'avons donné de ton propre fonds.
“Amma wane ni, kuma wace ce jama’ata da za mu iya ba ka a yalwace kamar haka? Kome daga gare ka suka fito, kuma mun ba ka abin da kawai ya fito daga hannunka ne.
15 Car nous sommes étrangers devant vous et étrangers, comme l'ont été tous nos pères. Nos jours sur la terre sont comme une ombre, et il n'y a pas de reste.
Mu bare ne kuma baƙi a gabanka, kamar yadda dukan kakanninmu suke. Kwanakinmu a duniya suna kamar inuwa ne, ba sa zuciya.
16 Yahvé notre Dieu, tout ce que nous avons préparé pour te bâtir une maison pour ton saint nom vient de ta main et t'appartient en propre.
Ya Ubangiji Allahnmu, game da dukan wannan yalwar da ka tanada saboda ginin haikali saboda Sunanka Mai Tsarki, sun fito daga hannunka ne, kuma dukan naka ne.
17 Je sais aussi, mon Dieu, que tu éprouves le cœur et que tu prends plaisir à la droiture. Moi, dans la droiture de mon cœur, j'ai offert volontairement toutes ces choses. Maintenant, j'ai vu avec joie ton peuple, qui est ici présent, t'offrir volontairement.
Na sani, Allahna, cewa kakan gwada zuciya, kakan kuma gamsu da mutunci. Dukan waɗannan abubuwa na bayar da yardar rai da kuma kyakkyawar niyya. Yanzu kuma da farin ciki na ga yadda mutanenka waɗanda suke a nan da yardar rai suka ba ka.
18 Yahvé, Dieu d'Abraham, d'Isaac et d'Israël, nos pères, garde ce désir à jamais dans les pensées du cœur de ton peuple, et prépare son cœur pour toi;
Ya Ubangiji Allah na kakanninmu Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, ka sa wannan sha’awa a cikin zukatan mutanenka har abada, ka kuma bar zukatansu su yi maka biyayya.
19 et donne à Salomon, mon fils, un cœur parfait, pour qu'il observe tes commandements, tes témoignages et tes statuts, qu'il fasse toutes ces choses et qu'il bâtisse le palais pour lequel j'ai pris des dispositions. »
Ka kuma ba ɗana Solomon cikakkiyar zuciya don yă kiyaye umarnanka, farillanka da ƙa’idodinka yă kuma yi kome don yă gina ƙasaitaccen gini wanda na riga na yi tanadi dominsa.”
20 Et David dit à toute l'assemblée: « Maintenant, bénissez Yahvé votre Dieu! » Toute l'assemblée bénit l'Éternel, le Dieu de leurs pères, et ils inclinèrent la tête et se prosternèrent devant l'Éternel et le roi.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa dukan taron, “Ku yabi Ubangiji Allahnku.” Saboda haka suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu; suka rusuna suka kuma fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji da kuma sarki.
21 Ils offrirent des sacrifices et des holocaustes à Yahvé le lendemain de ce jour, mille taureaux, mille béliers et mille agneaux, avec leurs libations et leurs sacrifices en abondance pour tout Israël,
Kashegari suka miƙa hadayu ga Ubangiji suka kuma miƙa hadayu bijimai dubu, raguna dubu da kuma’yan raguna dubu na ƙonawa gare shi, tare da hadayunsu na sha da sauran hadayu a yalwace saboda dukan Isra’ila.
22 et ils mangèrent et burent devant Yahvé ce jour-là avec une grande joie. Ils établirent roi pour la seconde fois Salomon, fils de David, et ils l'oignirent devant Yahvé comme prince, et Zadok comme sacrificateur.
Suka ci suka sha da farin ciki mai girma a gaban Ubangiji a wannan rana. Sa’an nan suka yarda da Solomon ɗan Dawuda a matsayin sarki sau na biyu, suka shafe shi a gaban Ubangiji don yă zama mai mulki, Zadok kuwa ya zama firist.
23 Salomon s'assit sur le trône de Yahvé comme roi à la place de David, son père, et il prospéra, et tout Israël lui obéit.
Saboda haka Solomon ya zauna a kujerar sarautar Ubangiji a matsayin sarki a maimakon mahaifinsa Dawuda. Ya yi nasara, dukan Isra’ila kuwa suka yi masa biyayya.
24 Tous les princes, les puissants, et aussi tous les fils du roi David se soumirent au roi Salomon.
Dukan shugabanni da jarumawa, har ma da dukan’ya’yan Sarki Dawuda maza, suka yi alkawari za su yi wa Sarki Solomon biyayya.
25 Yahvé magnifia Salomon aux yeux de tout Israël et lui donna une majesté royale telle qu'il n'y en avait eu aucune avant lui en Israël.
Ubangiji ya ɗaukaka Solomon sosai a idon dukan Isra’ila, ya kuma ba shi darajar sarauta yadda babu sarki a Isra’ilan da ya taɓa samu.
26 David, fils d'Isaï, régna sur tout Israël.
Dawuda ɗan Yesse ya zama sarki a bisa dukan Isra’ila.
27 Le temps qu'il régna sur Israël fut de quarante ans; il régna sept ans à Hébron, et il régna trente-trois ans à Jérusalem.
Ya yi mulki a bisa Isra’ila shekaru arba’in, shekaru bakwai a Hebron da kuma shekaru talatin da uku a Urushalima.
28 Il mourut dans une belle vieillesse, rassasié de jours, de richesses et de gloire; et Salomon, son fils, régna à sa place.
Ya mutu a kyakkyawar tsufa, bayan ya more dogon rai, wadata da girma. Ɗansa Solomon ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Les actes du roi David, les premiers et les derniers, sont écrits dans l'histoire de Samuel le voyant, dans l'histoire de Nathan le prophète, et dans l'histoire de Gad le voyant,
Game da ayyukan mulkin Sarki Dawuda, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin Sama’ila mai duba, tarihin annabi Natan da kuma tarihin Gad mai duba,
30 avec tout son règne et sa puissance, et les événements qui l'ont impliqué, lui, Israël, et tous les royaumes des pays.
tare da yadda mulkinsa da ikonsa da yanayin da suka kewaye shi da Isra’ila da kuma dukan masarautai na dukan sauran ƙasashe.

< 1 Chroniques 29 >