< 1 Chroniques 16 >

1 Ils firent entrer l'arche de Dieu et la placèrent au milieu de la tente que David avait dressée pour elle, et ils offrirent devant Dieu des holocaustes et des sacrifices de prospérité.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 Lorsque David eut achevé d'offrir les holocaustes et les sacrifices de prospérité, il bénit le peuple au nom de l'Éternel.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 Il donna à tous ceux d'Israël, hommes et femmes, un pain, une portion de viande et un gâteau de raisins secs.
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 Il désigna quelques-uns des Lévites pour faire le service devant l'arche de l'Éternel, pour commémorer, remercier et louer l'Éternel, le Dieu d'Israël:
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph, le chef, et après lui Zacharie, puis Jeïel, Schemiramoth, Jehiel, Mattithia, Éliab, Benaja, Obed-Édom et Jeïel, avec des instruments à cordes et des harpes; Asaph, avec des cymbales, en sonnant à haute voix;
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 et les sacrificateurs Benaja et Jahaziel, avec des trompettes, toujours devant l'arche de l'alliance de Dieu.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Et en ce jour-là, David ordonna pour la première fois de rendre grâce à Yahvé par l'intermédiaire d'Asaph et de ses frères.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 Oh! Rendez grâce à Yahvé. Invoquez son nom. Faites connaître ce qu'il a fait parmi les peuples.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Chantez pour lui. Chantez-lui des louanges. Racontez toutes ses œuvres merveilleuses.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Gloire à son saint nom. Que le cœur de ceux qui cherchent Yahvé se réjouisse.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Cherchez Yahvé et sa force. Cherchez son visage pour toujours.
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Souvenez-vous des merveilles qu'il a faites, ses merveilles, et les jugements de sa bouche,
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 vous, progéniture d'Israël, son serviteur, vous, enfants de Jacob, ses élus.
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 Il est Yahvé, notre Dieu. Ses jugements sont dans toute la terre.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Souviens-toi de son alliance pour toujours, la parole qu'il a commandée à mille générations,
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 l'alliance qu'il a conclue avec Abraham, son serment à Isaac.
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 Il le confirma à Jacob comme une loi, et à Israël pour une alliance éternelle,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 en disant: « Je te donnerai le pays de Canaan, Le lot de votre héritage, »
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 quand vous n'étiez qu'un petit nombre d'hommes, oui, très peu, et des étrangers en son sein.
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 Ils allaient de nation en nation, d'un royaume à un autre peuple.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 Il n'a permis à personne de leur faire du tort. Oui, il a réprimandé les rois pour leur bien,
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 « Ne touchez pas à mes oints! Ne faites pas de mal à mes prophètes! »
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Chantez à Yahvé, toute la terre! Afficher son salut au jour le jour.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 Déclarez sa gloire parmi les nations, et ses merveilles parmi tous les peuples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 Car Yahvé est grand et digne de louange. Il doit également être craint par-dessus tous les dieux.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 Car tous les dieux des peuples sont des idoles, mais Yahvé a fait les cieux.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 L'honneur et la majesté sont devant lui. La force et la joie sont à sa place.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Rendez hommage à Yahvé, vous, familles des peuples, attribue à Yahvé la gloire et la force!
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Rendez à Yahvé la gloire due à son nom. Apportez une offrande, et venez devant lui. Adorez Yahvé dans une tenue sacrée.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Tremblez devant lui, toute la terre! Le monde est également établi qu'il ne peut pas être déplacé.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Que les cieux se réjouissent! et que la terre se réjouisse! Qu'ils disent parmi les nations: « Yahvé règne! »
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 Que la mer rugisse, et sa plénitude! Que le champ exulte, et tout ce qu'il contient!
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Alors les arbres de la forêt chanteront de joie devant Yahvé, car il vient pour juger la terre.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 Oh! Rendez grâce à Yahvé, car il est bon, car sa bonté est éternelle.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 Dis: « Sauve-nous, Dieu de notre salut! Rassemblez-nous et délivrez-nous des nations, pour rendre grâce à ton saint nom, pour triompher dans ta louange. »
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Béni soit Yahvé, le Dieu d'Israël, de l'éternité à l'éternité. Tout le peuple dit: « Amen » et loua Yahvé.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 Il laissa là Asaph et ses frères devant l'arche de l'alliance de Yahvé, pour qu'ils fassent le service devant l'arche continuellement, selon le travail de chaque jour;
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 et Obed-Edom avec leurs soixante-huit parents; Obed-Edom aussi, fils de Jeduthun, et Hosah pour être portiers;
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 et le sacrificateur Zadok et ses frères les sacrificateurs, devant la tente de Yahvé, dans le haut lieu qui était à Gabaon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 pour offrir des holocaustes à Yahvé sur l'autel des holocaustes, continuellement, matin et soir, selon tout ce qui est écrit dans la loi de Yahvé, qu'il a prescrite à Israël;
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 Avec eux, Héman et Jeduthun, et les autres élus nommément désignés, pour rendre grâces à l'Éternel, parce que sa miséricorde dure à toujours.
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 Avec eux, Héman et Jeduthun, avec des trompettes et des cymbales pour ceux qui doivent sonner à haute voix, et avec des instruments pour les chants de Dieu, et les fils de Jeduthun pour être à la porte.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 Tout le peuple partit, chacun dans sa maison, et David s'en retourna pour bénir sa maison.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.

< 1 Chroniques 16 >