< Psalmien 62 >
1 Veisuunjohtajalle; Jedutunin tapaan; Daavidin virsi. Jumalaa yksin minun sieluni hiljaisuudessa odottaa, häneltä tulee minulle apu.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 Hän yksin on minun kallioni, minun apuni ja turvani: en minä suuresti horju.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 Kuinka kauan te yhtä miestä ahdistatte, hänet yhdessä surmataksenne, niinkuin hän olisi kaatuva seinä, niinkuin murrettu muuri?
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 He vain pitävät neuvoa, miten syöstä hänet korkeudestaan. He rakastavat valhetta, he siunaavat suullansa ja kiroavat sydämessänsä. (Sela)
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 Odota yksin Jumalaa hiljaisuudessa, minun sieluni, sillä häneltä tulee minun toivoni.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 Hän yksin on minun kallioni, minun apuni ja turvani: en minä horju.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 Jumalassa on minun apuni ja kunniani. Minun väkevyyteni kallio, minun turvani on Jumala.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Turvatkaa häneen joka aika, te kansa; vuodattakaa hänen eteensä sydämenne. Jumala on meidän turvamme. (Sela)
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 Vain tuulen henkäystä ovat ihmiset, vain valhetta ihmisten lapset: kaikki he nousevat vaa'assa ylös köykäisempinä kuin tuulenhenkäys.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 Älkää luottako väkivaltaan, älkää turhaan panko toivoanne ryöstettyyn tavaraan. Jos rikkautta karttuu, älkää siihen sydäntänne kiinnittäkö.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 Kerran on Jumala sanonut, kahdesti olen sen kuullut: väkevyys on Jumalan.
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 Ja sinun, Herra, on armo; sillä sinä maksat kullekin hänen tekojensa mukaan.
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”