< Psalmien 39 >

1 Veisuunjohtajalle; Jedutunin tapaan; Daavidin virsi. Minä sanoin: "Minä pidän vaelluksestani vaarin, etten kielelläni syntiä tekisi. Minä pidän suustani vaarin ja suistan sen, niin kauan kuin jumalaton on minun edessäni."
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zabura ta Dawuda. Na ce, “Zan lura da hanyoyina zan kuma kiyaye harshena daga zunubi; zan sa linzami a bakina muddin mugaye suna a gabana.”
2 Minä olin vaiti, olin ääneti, en puhunut siitä, mikä hyvä on; mutta minun tuskani yltyi.
Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi;
3 Minun sydämeni hehkui minun rinnassani; kun minä huokailin, syttyi minussa tuli, ja niin minä kielelläni puhuin.
zuciyata ta ƙara zafi a cikina. Kuma sa’ad da nake tunani, wuta ta yi ta kuna; sai na yi magana da harshena na ce,
4 Herra, opeta minua ajattelemaan loppuani, ja mikä minun päivieni mitta on, että ymmärtäisin, kuinka katoavainen minä olen.
“Nuna mini, ya Ubangiji, ƙarshen rayuwata da kuma yawan kwanakina; bari in san yadda rayuwata tana wucewa da sauri.
5 Katso, kämmenen leveydeksi sinä teit minun päiväni, ja minun elämäni on sinun edessäsi niinkuin ei mitään. Vain tuulen henkäys ovat kaikki ihmiset, kuinka lujina seisokootkin. (Sela)
Ka sa kwanakina suka zama tafin hannu ne kawai; yawan shekaruna kamar ba kome ba ne a gabanka. Duk ran mutum shaƙar iska ne kurum, har ma waɗanda suke tsammani suke da kāriya. (Sela)
6 Varjona vain ihminen vaeltaa, turhaan vain he touhuavat, kokoavat, eivätkä tiedä, kuka ne saa.
“Mutum dai shirim ne kawai yayinda yake kai da komowa. Yana ta yawo, amma a banza ne kawai; yakan tara dukiya, ba tare da sanin wa zai more ta ba.
7 Ja nyt, mitä minä odotan, Herra? Sinuun minä panen toivoni.
“Amma yanzu, ya Ubangiji, me zan nema? Begena yana a gare ka.
8 Päästä minut kaikista synneistäni, älä pane minua houkkain pilkaksi.
Ka cece ni daga dukan laifofina; kada ka sa in zama abin dariya ga wawaye.
9 Minä vaikenen enkä suutani avaa; sillä sinä sen teit.
Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
10 Käännä vitsauksesi minusta pois, sillä minä menehdyn sinun kätesi kuritukseen.
Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.
11 Kun sinä ihmistä synnin tähden rangaistuksilla kuritat, kulutat sinä hänen kauneutensa niinkuin koinsyömän. Vain tuulen henkäys ovat kaikki ihmiset. (Sela)
Kakan tsawata ka kuma hore mutane saboda zunubinsu; kakan cinye wadatarsu kamar yadda asu ke yi, kowane mutum dai shaƙar iska ne. (Sela)
12 Kuule minun rukoukseni, Herra, ota korviisi minun huutoni. Älä ole kuuro minun kyyneleilleni; sillä minä olen muukalainen sinun tykönäsi, vieras, niinkuin kaikki minun isänikin.
“Ka ji addu’ata, ya Ubangiji, ka saurari kukata ta neman taimako; kada ka kurmance ga kukata. Gama ina zama tare da kai kamar baƙo, baƙo, kamar yadda dukan kakannina sun kasance.
13 Käännä pois katseesi minusta, että minä ilostuisin, ennenkuin menen pois eikä minua enää ole.
Ka kau da fuskarka daga gare ni, saboda in sāke yin farin ciki kafin in tafi in kuma rabu da nan.”

< Psalmien 39 >