< Psalmien 137 >
1 Baabelin virtain vierillä-siellä me istuimme ja itkimme, kun Siionia muistelimme.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 Pajuihin, joita siellä oli, me ripustimme kanteleemme.
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 Sillä vangitsijamme vaativat meiltä siellä lauluja ja orjuuttajamme iloa: "Veisatkaa meille Siionin virsiä".
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 Kuinka me voisimme veisata Herran virsiä vieraalla maalla?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 Jos minä unhotan sinut, Jerusalem, niin unhota sinä minun oikea käteni.
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Tarttukoon kieleni suuni lakeen, ellen minä sinua muista, ellen pidä Jerusalemia ylimpänä ilonani.
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Muista, Herra, Jerusalemin tuhopäivä, kosta se Edomin lapsille, jotka sanoivat: "Hajottakaa se, hajottakaa perustuksia myöten!"
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Tytär Baabel, sinä häviön oma, autuas se, joka sinulle kostaa kaiken, minkä olet meille tehnyt!
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Autuas se, joka ottaa sinun pienet lapsesi ja murskaa ne kallioon!
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.