< Psalmien 130 >

1 Matkalaulu. Syvyydestä minä huudan sinua, Herra.
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Herra, kuule minun ääneni. Tarkatkoot sinun korvasi minun rukousteni ääntä.
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Jos sinä, Herra, pidät mielessäsi synnit, Herra, kuka silloin kestää?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Mutta sinun tykönäsi on anteeksiantamus, että sinua peljättäisiin.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 Minä odotan Herraa, minun sieluni odottaa, ja minä panen toivoni hänen sanaansa.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 Minun sieluni odottaa Herraa hartaammin kuin vartijat aamua, kuin vartijat aamua.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Pane toivosi Herraan, Israel. Sillä Herran tykönä on armo, runsas lunastus hänen tykönänsä.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 Ja hän lunastaa Israelin kaikista sen synneistä.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalmien 130 >