< Jobin 4 >
1 Silloin teemanilainen Elifas lausui ja sanoi:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 "Ethän pane pahaksesi, jos sinulle puhutaan? Kuka voi vaitikaan olla?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Katso, monta sinä olet ojentanut, ja hervonneita käsiä olet vahvistanut;
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 sanasi ovat nostaneet kompastunutta, ja rauenneita polvia olet voimistanut.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 Mutta nyt, kun itseäsi kova kohtaa, sinä tuskastut, kun se sinuun sattuu, sinä kauhistut.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Eikö jumalanpelkosi ole sinun uskalluksesi ja nuhteeton vaelluksesi sinun toivosi?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Ajattele, kuka viaton on koskaan hukkunut, ja missä ovat rehelliset joutuneet perikatoon?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 Minkä minä olen nähnyt, niin ne, jotka vääryyttä kyntävät ja turmiota kylvävät, ne sitä niittävätkin.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 Jumalan henkäyksestä he hukkuvat, hänen vihansa hengestä he häviävät.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 Leijonan ärjyntä, jalopeuran ääni vaiennetaan, ja nuorten leijonain hampaat murskataan;
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 jalopeura menehtyy saaliin puutteesta, ja naarasleijonan pennut hajaantuvat.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 Ja minulle tuli salaa sana, korvani kuuli kuiskauksen,
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 kun ajatukset liikkuivat öisissä näyissä, kun raskas uni oli vallannut ihmiset.
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 Pelko ja vavistus yllättivät minut, peljästyttivät kaikki minun luuni.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Tuulen henkäys hiveli kasvojani, ihoni karvat nousivat pystyyn.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 Siinä seisoi-sen näköä en erottanut-haamu minun silmäini edessä; minä kuulin kuiskaavan äänen:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 'Onko ihminen vanhurskas Jumalan edessä, onko mies Luojansa edessä puhdas?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Katso, palvelijoihinsakaan hän ei luota, enkeleissäänkin hän havaitsee vikoja;
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 saati niissä, jotka savimajoissa asuvat, joiden perustus on maan tomussa! He rusentuvat kuin koiperhonen;
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 ennenkuin aamu ehtooksi muuttuu, heidät muserretaan. Kenenkään huomaamatta he hukkuvat ainiaaksi.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 Eikö niin: heidän telttanuoransa irroitetaan, ja he kuolevat, viisaudesta osattomina.'"
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’