< Jesajan 65 >

1 Minä olen suostunut niiden etsittäväksi, jotka eivät minua kysyneet, niiden löydettäväksi, jotka eivät minua etsineet; minä olen sanonut kansalle, joka ei ole otettu minun nimiini: Tässä minä olen, tässä minä olen!
“Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
2 Koko päivän minä olen ojentanut käsiäni uppiniskaista kansaa kohden, joka vaeltaa tietä, mikä ei ole hyvä, omain ajatustensa mukaan;
Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
3 kansaa kohden, joka vihoittaa minua alinomaa, vasten kasvojani, uhraa puutarhoissa ja suitsuttaa tiilikivialttareilla.
mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
4 He asustavat haudoissa ja yöpyvät salaisiin paikkoihin; he syövät sianlihaa, ja saastaiset liemet on heillä astioissansa.
suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
5 He sanovat: "Pysy erilläsi, älä tule minua lähelle, sillä minä olen sinulle pyhä". Nämä ovat savu minun sieramissani, tuli, joka palaa kaiken päivää.
suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
6 Katso, se on kirjoitettuna minun edessäni. En ole minä vaiti, vaan minä maksan, maksan heille helmaan
“Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
7 heidän pahat tekonsa ynnä teidän isienne pahat teot, sanoo Herra, niiden, jotka ovat vuorilla suitsuttaneet ja kukkuloilla minua häväisseet; ja ensiksi minä mittaan heille palkan heidän helmaansa.
saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
8 Näin sanoo Herra: Niinkuin sanotaan rypäleestä, jos siinä on mehua: "Älä hävitä sitä, sillä siinä on siunaus", niin teen minä palvelijaini tähden, etten kaikkea hävittäisi.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
9 Minä tuotan Jaakobista siemenen ja Juudasta vuorteni perillisen; ja minun valittuni saavat periä maan, ja minun palvelijani saavat siinä asua.
Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
10 Ja Saaron on oleva lammasten laitumena ja Aakorin laakso karjan lepopaikkana minun kansallani, joka minua etsii.
Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
11 Mutta te, jotka hylkäätte Herran ja unhotatte minun pyhän vuoreni, jotka valmistatte Gadille pöydän ja vuodatatte uhrijuomaa Menille-
“Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
12 teidät minä määrään miekan omiksi, ja kaikki te kumarrutte teurastettaviksi, sentähden ettette vastanneet, kun minä kutsuin, ettekä kuulleet, kun minä puhuin, vaan teitte sitä, mikä on pahaa minun silmissäni, ja valitsitte sen, mikä ei ole minulle otollista.
zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
13 Sentähden, näin sanoo Herra, Herra: Katso, minun palvelijani syövät, mutta te näette nälkää; katso, minun palvelijani juovat, mutta te kärsitte janoa; katso, minun palvelijani iloitsevat, mutta te joudutte häpeään.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
14 Katso, minun palvelijani riemuitsevat sydämen onnesta, mutta te huudatte sydämen tuskasta ja voivotatte mielimurteissanne.
Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
15 Ja te jätätte nimenne kirouslauseeksi minun valituilleni: "Niin sinut surmatkoon Herra, Herra!" Mutta palvelijoilleen hän on antava toisen nimen.
Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
16 Joka maassa itsensä siunaa, siunaa itsensä totisen Jumalan nimeen, ja joka maassa vannoo, vannoo totisen Jumalan nimeen; sillä entiset ahdistukset ovat unhotetut ja peitossa minun silmiltäni.
Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
17 Sillä katso, minä luon uudet taivaat ja uuden maan. Entisiä ei enää muisteta, eivätkä ne enää ajatukseen astu;
“Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
18 vaan te saatte iloita ja riemuita iankaikkisesti siitä, mitä minä luon. Sillä katso, iloksi luon minä Jerusalemin, riemuksi sen kansan.
Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
19 Minä iloitsen Jerusalemista ja riemuitsen kansastani; eikä siellä enää kuulla itkun ääntä eikä valituksen ääntä.
Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
20 Ei siellä ole enää lasta, joka eläisi vain muutaman päivän, ei vanhusta, joka ei täyttäisi päiviensä määrää; sillä nuorin kuolee satavuotiaana, ja vasta satavuotiaana synnintekijä joutuu kiroukseen.
“A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
21 He rakentavat taloja ja asuvat niissä, he istuttavat viinitarhoja ja syövät niiden hedelmät;
Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
22 he eivät rakenna muitten asua, eivät istuta muitten syödä; sillä niinkuin puitten päivät ovat, niin ovat elinpäivät minun kansassani. Minun valittuni kuluttavat itse kättensä työn.
Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
23 He eivät tee työtä turhaan eivätkä lapsia synnytä äkkikuoleman omiksi, sillä he ovat Herran siunattujen siemen, ja heidän vesansa ovat heidän tykönänsä.
Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
24 Ennenkuin he huutavat, minä vastaan, heidän vielä puhuessaan minä kuulen.
Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
25 Susi ja lammas käyvät yhdessä laitumella, ja leijona syö rehua niinkuin raavas, ja käärmeen ruokana on maan tomu; ei missään minun pyhällä vuorellani tehdä pahaa eikä vahinkoa, sanoo Herra.
Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.

< Jesajan 65 >