< Jesajan 49 >

1 Kuulkaa minua, te merensaaret, ja tarkatkaa, kaukaiset kansat. Herra on minut kutsunut hamasta äidinkohdusta saakka, hamasta äitini helmasta minun nimeni maininnut.
Ku kasa kunne gare ni, ku tsibirai; ku ji wannan, ku al’ummai masu nesa. Kafin a haife Ni Ubangiji ya kira ni; tun daga haihuwata ya ambaci sunana.
2 Hän teki minun suuni terävän miekan kaltaiseksi, kätki minut kätensä varjoon; hän teki minut hiotuksi nuoleksi, talletti minut viineensä.
Ya yi bakina kamar takobi mai kaifi, cikin inuwar hannunsa ya ɓoye ni; ya sa na zama kamar kibiya mai tsini ya kuma ɓoye ni cikin kwarinsa.
3 Ja hän sanoi minulle: "Sinä olet minun palvelijani, sinä Israel, jossa minä osoitan kirkkauteni".
Ya ce mini, “Kai bawana ne, Isra’ila, a cikinka zan bayyana darajata.”
4 Mutta minä sanoin: "Hukkaan minä olen itseäni vaivannut, kuluttanut voimani turhaan ja tyhjään; kuitenkin on minun oikeuteni Herran huomassa, minun palkkani on Jumalan tykönä".
Amma na ce, “Na yi aiki a banza; na kashe duk ƙarfina a banza da wofi. Duk da haka abin da yake nawa yana a hannun Ubangiji, ladana kuma tana a wurin Allahna.”
5 Ja nyt sanoo Herra, joka on minut palvelijakseen valmistanut hamasta äitini kohdusta, palauttamaan Jaakobin hänen tykönsä, niin että Israel koottaisiin hänen omaksensa-ja minä olen kallis Herran silmissä, minun Jumalani on tullut minun voimakseni-
Yanzu fa Ubangiji ya ce ya siffanta ni a cikin mahaifa don in zama bawansa don in dawo da Yaƙub gare shi in kuma tattara Isra’ila gare shi, gama an girmama ni a gaban Ubangiji Allahna kuma ne ƙarfina
6 hän sanoo: Liian vähäistä on sinulle, joka olet minun palvelijani, kohottaa ennalleen Jaakobin sukukunnat ja tuoda takaisin Israelin säilyneet: minä panen sinut pakanain valkeudeksi, että minulta tulisi pelastus maan ääriin asti.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
7 Näin sanoo Herra, Israelin lunastaja, hänen Pyhänsä, syvästi halveksitulle, kansan inhoamalle, valtiaitten orjalle: Kuninkaat näkevät sen ja nousevat seisomaan, ruhtinaat näkevät ja kumartuvat maahan Herran tähden, joka on uskollinen, Israelin Pyhän tähden, joka on sinut valinnut.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansa da kuma Mai Tsarkin nan na Isra’ila gare shi wanda al’ummai suka rena suka kuma ki, ga bawan masu mulki. “Sarakuna za su gan ka su kuma miƙe tsaye, sarakuna za su gani su kuma rusuna, saboda Ubangiji, wanda yake mai aminci, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, wanda ya zaɓe ka.”
8 Näin sanoo Herra: Otollisella ajalla minä olen sinua kuullut ja pelastuksen päivänä sinua auttanut; minä olen valmistanut sinut ja pannut sinut kansoille liitoksi, kohottamaan ennalleen maan, jakamaan hävitetyt perintöosat,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “A lokacin tagomashina zan amsa muku, kuma a ranar ceto zan taimake ku; zan kiyaye ku zan kuma sa ku zama alkawari ga mutane, don ku maido da ƙasa ku kuma sāke raba gādon kufai,
9 sanomaan vangituille: "Käykää ulos!" ja pimeässä oleville: "Tulkaa esiin!" Teiden varsilta he löytävät laitumen, kaikki kalliokukkulat ovat heillä laidunpaikkoina.
don ku ce wa waɗanda suke cikin kurkuku, ‘Ku fito,’ ga waɗanda suke cikin duhu kuma, ‘Ku’yantu!’ “Za su yi kiwo kusa da hanyoyi su kuma sami wurin kiwo a kowane tudu.
10 Ei heidän tule nälkä eikä jano, ei hietikon helle eikä aurinko satu heihin, sillä heidän armahtajansa johdattaa heitä ja vie heidät vesilähteille.
Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba, ba kuwa zafin hamada ko rana ta buge su ba. Shi da ya yi musu jinƙai zai jagorance su ya kuma bishe su kusa da maɓulɓulan ruwa.
11 Minä teen kaikki vuoreni teiksi, ja minun valtatieni kulkevat korkealla.
Zan mayar da dukan duwatsu su zama hanyoyi, a kuma gyara manyan hanyoyina.
12 Katso heitä, he tulevat kaukaa! Katso, nuo pohjoisesta, nuo lännestä, nuo Siinimin maalta!
Duba, za su zo daga nesa waɗansu daga arewa, waɗansu daga yamma, waɗansu daga yankin Aswan.”
13 Riemuitkaa, te taivaat, iloitse, sinä maa, puhjetkaa riemuun, te vuoret, sillä Herra lohduttaa kansaansa ja armahtaa kurjiansa.
Ku yi sowa don farin ciki, ya ku sammai; ki yi farin ciki, ya ke duniya; ku ɓarke da waƙa, ya ku duwatsu! Gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa zai kuma ji tausayin mutanensa da suke shan wahala.
14 Mutta Siion sanoo: "Herra on minut hyljännyt, Herra on minut unhottanut".
Amma Sihiyona ta ce, “Ubangiji ya yashe ni, Ubangiji ya manta da ni.”
15 Unhottaako vaimo rintalapsensa, niin ettei hän armahda kohtunsa poikaa? Ja vaikka he unhottaisivatkin, minä en sinua unhota.
“Yana yiwuwa mahaifiya ta manta da jariri a ƙirjinta ta kuma kāsa nuna tausayi ga yaron da ta haifa? Mai yiwuwa ta manta, amma ba zan taɓa manta da ke ba!
16 Katso, kätteni hipiään olen minä sinut piirtänyt, sinun muurisi ovat aina minun edessäni.
Duba, na zāna ki a tafin hannuwana; katangarki kullum suna a gabana.
17 Sinun lapsesi tulevat rientäen; sinun hävittäjäsi ja raunioiksi-raastajasi menevät sinun luotasi pois.
’Ya’yanki maza su komo da gaggawa, waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su bar ki.
18 Nosta silmäsi ja katso ympärillesi: he kokoontuvat, he tulevat sinun tykösi kaikki. Niin totta kuin minä elän, sanoo Herra, sinä puet heidät kaikki yllesi niinkuin koristeen ja sidot heidät vyöllesi niinkuin morsian vyönsä.
Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye; dukan’ya’yanki sun taru suka kuma dawo gare ki. Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “Za ki yafa su duka kamar kayan ado; za ki yi ado da su, kamar amarya.
19 Sillä sinä-sinun rauniosi ja autiot paikkasi, sinun hävitetty maasi-sinä käyt silloin ahtaaksi asukkaille, ja kaukana ovat ne, jotka sinua söivät.
“Ko da yake an lalatar da ke aka kuma mai da ke kufai ƙasarki kuma ta zama kango, yanzu za ki kāsa sosai saboda yawan mutanenki, kuma waɗanda suka cinye ki za su kasance can da nisa.
20 Vielä saavat sinun lapsettomuutesi lapset sanoa korviesi kuullen: "Paikka on minulle ahdas, tee tilaa, että voin asua".
’Ya’yan da aka haifa a lokacin baƙin cikinki za su ce a kunnenki, ‘Wannan wuri ya yi mana kaɗan ƙwarai; ki ƙara mana wurin zama.’
21 Silloin sinä sanot sydämessäsi: "Kuka on nämä minulle synnyttänyt? Minä olin lapseton ja hedelmätön, karkoitettu ja hyljätty. Kuka on heidät kasvattanut? Katso, minä olin jätetty yksin. Missä nämä silloin olivat?
Sa’an nan za ki ce a zuciyarki, ‘Wa ya haifa waɗannan? Na yi baƙin ciki na kuma zama wadda ba ta haihuwa; an yi mini daurin talala aka kuma ƙi ni. Wane ne ya yi renon waɗannan? An bar ni ni kaɗai, amma waɗannan, ina suka fito?’”
22 Näin sanoo Herra, Herra: Katso, minä nostan käteni kansakuntien puoleen, kohotan lippuni kansoja kohti, niin he tuovat sinun poikasi sylissänsä ja kantavat sinun tyttäresi olkapäillään.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe’ya’yanki mata a kafaɗunsu.
23 Kuninkaista tulee sinulle lastenhoitajat, heidän ruhtinattaristaan sinulle imettäjät. Sinun edessäsi he kumartuvat maahan kasvoillensa ja nuolevat tomun sinun jaloistasi. Silloin sinä tiedät, että minä olen Herra ja että ne, jotka minua odottavat, eivät häpeään joudu.
Sarakuna za su zama kamar iyayen reno, sarauniyoyinsu kuma za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna a gabanki da fuskokinsu har ƙasa; za su lashe ƙura a ƙafafunki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji; waɗanda suke sa zuciya gare ni ba za su sha kunya ba.”
24 Otetaanko sankarilta saalis, tai riistetäänkö vangit vanhurskaalta?
Za a iya ƙwace ganima daga jarumawa, ko a kuɓutar da kamammu daga hannun marasa tsoro?
25 Sillä näin sanoo Herra: Vaikka vangit otettaisiinkin sankarilta ja saalis riistettäisiin väkevältä, niin minä kuitenkin taistelen sitä vastaan, joka sinua vastaan taistelee, ja minä pelastan sinun lapsesi.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci’ya’yanki.
26 Minä panen sinun sortajasi syömään omaa lihaansa, ja he juopuvat omasta verestään niinkuin rypälemehusta; ja kaikki liha on tietävä, että minä, Herra, olen sinun pelastajasi, että Jaakobin Väkevä on sinun lunastajasi.
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”

< Jesajan 49 >