< Jesajan 39 >
1 Siihen aikaan Merodak-Baladan, Baladanin poika, Baabelin kuningas, lähetti kirjeen ja lahjoja Hiskialle, kun oli kuullut hänen olleen sairaana ja parantuneen.
A wannan lokaci Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu da kuma kyauta, domin ya ji rashin lafiyarsa da kuma warkarwarsa.
2 Ja Hiskia iloitsi lähettiläistä ja näytti heille varastohuoneensa, hopean ja kullan, hajuaineet ja kalliin öljyn ja koko asehuoneensa ja kaikki, mitä hänen aarrekammioissansa oli. Ei ollut mitään Hiskian talossa eikä koko hänen valtakunnassaan, mitä hän ei olisi heille näyttänyt.
Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
3 Mutta profeetta Jesaja tuli kuningas Hiskian tykö ja sanoi hänelle: "Mitä nämä miehet ovat sanoneet, ja mistä he ovat tulleet sinun tykösi?" Hiskia vastasi: "He ovat tulleet minun tyköni kaukaisesta maasta, Baabelista".
Sai Ishaya annabi ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi ya ce, “Mene ne waɗannan mutane suka faɗa, kuma daga ina suka fito?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Sun zo ne daga Babilon.”
4 Hän sanoi: "Mitä he ovat nähneet sinun talossasi?" Hiskia vastasi: "Kaiken, mitä talossani on, he ovat nähneet; aarrekammiossani ei ole mitään, mitä en olisi heille näyttänyt".
Annabi ya yi tambaya ya ce, “Mene ne suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga kome da kome a fadana. Babu abin da ban nuna musu a cikin ma’ajina ba.”
5 Niin Jesaja sanoi Hiskialle: "Kuule Herran Sebaotin sana:
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji maganar Ubangiji Maɗaukaki.
6 Katso, päivät tulevat, jolloin kaikki, mitä sinun talossasi on ja mitä sinun isäsi ovat koonneet tähän päivään asti, viedään pois Baabeliin; ei mitään jää jäljelle, sanoo Herra.
Tabbatacce lokaci yana zuwa sa’ad da kome da yake cikin fadanka, da kuma dukan abin da kakanninka suka ajiye har yă zuwa yau, za a kwashe zuwa Babilon babu abin da za a bari, in ji Ubangiji.
7 Ja sinun omia poikiasi, jotka sinusta polveutuvat, jotka sinulle syntyvät, viedään hovipalvelijoiksi Baabelin kuninkaan palatsiin."
Waɗansu cikin zuriyarka, nama da jininka waɗanda za a haifa maka, za a kwashe su a tafi, za su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
8 Hiskia sanoi Jesajalle: "Herran sana, jonka olet puhunut, on hyvä". Sillä hän ajatteli: "Onpahan rauha ja turvallisuus minun päivinäni".
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka yi tana da kyau.” Gama ya yi tunani a ransa cewa, “Salama da kāriya za su kasance a zamanina.”