< Habakukin 1 >

1 Ennustus, jonka profeetta Habakuk näki.
Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
2 Kuinka kauan, Herra, minun täytyy apua huutaa, ja sinä et kuule, parkua sinulle: "Väkivaltaa!" ja sinä et auta?
Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
3 Minkätähden sinä annat minun nähdä vääryyttä ja itse katselet turmiota? Minun edessäni on hävitys ja väkivalta; on syntynyt riita, ja on noussut tora.
Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
4 Sentähden on laki heikko, ja oikeus ei tule milloinkaan voimaan. Sillä jumalaton saartaa vanhurskaan; sentähden oikeus vääristetään.
Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
5 Katsokaa kansojen joukkoon, katselkaa ja kauhistukaa, sillä minä teen teidän päivinänne teon, jota ette uskoisi, jos siitä kerrottaisiin.
“Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
6 Sillä katso, minä nostan kaldealaiset, tuiman ja rajun kansan, joka kulkee maata lavealti ja ottaa omaksensa asuinsijat, jotka eivät ole sen.
Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
7 Se on hirmuinen ja peljättävä, siitä itsestään tulee sen oikeus ja sen korkeus.
Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
8 Sen hevoset ovat nopeammat kuin pantterit, ne juoksevat kiivaammin kuin sudet illoin. Sen ratsumiehet kiidättävät-kaukaa tulevat sen ratsumiehet, ne lentävät, niinkuin kotka syöksyy syönnökselleen.
Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
9 Se tulee kaikkinensa väkivallan tekoon, heidän kasvojensa suunta on suoraan eteenpäin; se kokoaa vankeja kuin hietaa.
duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
10 Pilkkanaan pitää se kuninkaat ja naurunansa ruhtinaat. Se nauraa kaikille varustuksille, kasaa kokoon hiekkaa ja valloittaa ne.
Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
11 Sitten se tuulena kiitää ja hyökkää, mutta joutuu syynalaiseksi, tuo, jolla oma voimansa on jumalana.
Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
12 Etkö sinä ole ikiajoista asti Herra, minun pyhä Jumalani? Me emme kuole! Sinä, Herra, olet pannut sen tuomioksi; sinä, kallio, olet asettanut sen kuritukseksi.
Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
13 Sinun silmäsi ovat puhtaat, niin ettet voi katsoa pahaa etkä saata katsella turmiota. Minkätähden sinä katselet uskottomia, olet vaiti, kun jumalaton nielee hurskaampansa,
Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
14 teet ihmiset samankaltaisiksi kuin meren kalat, kuin matelevaiset, joilla ei ole hallitsijaa?
Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
15 Se nostaa heidät kaikki ylös koukulla, vetää heidät pyydyksessään ja kokoaa heidät verkkoonsa. Sentähden se iloitsee ja riemuitsee.
Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
16 Sentähden se uhraa pyydykselleen ja polttaa uhreja verkollensa, sillä niitten turvin sen osa on rasvainen, sen ruoka lihava.
Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
17 Saako se sentähden tyhjentää pyydyksensä, aina surmata kansoja säälimättä?
Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?

< Habakukin 1 >