< 2 Mooseksen 19 >

1 Kolmantena kuukautena siitä, kun israelilaiset olivat lähteneet Egyptin maasta, juuri samana kuukauden päivänä, he tulivat Siinain erämaahan.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 Sillä he olivat lähteneet Refidimistä, tulleet Siinain erämaahan ja leiriytyneet erämaahan; ja Israel oli siellä leirissä vuoren kohdalla.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 Ja Mooses nousi Jumalan tykö, ja Herra huusi häntä vuorelta ja sanoi: "Sano näin Jaakobin heimolle ja ilmoita israelilaisille:
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 'Te olette nähneet, mitä minä olen tehnyt egyptiläisille ja kuinka minä olen kantanut teitä kotkan siivillä ja tuonut teidät luokseni.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 Jos te nyt kuulette minun ääntäni ja pidätte minun liittoni, niin te olette minun omaisuuteni ennen kaikkia muita kansoja; sillä koko maa on minun.
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 Ja te olette minulle pappisvaltakunta ja pyhä kansa.' Sano nämä sanat israelilaisille."
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 Kun Mooses tuli takaisin, kutsui hän kokoon kansan vanhimmat ja puhui heille kaikki ne sanat, jotka Herra oli hänen käskenyt puhua.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 Niin koko kansa vastasi yhtenä miehenä ja sanoi: "Kaiken, mitä Herra on puhunut, me teemme". Ja Mooses vei kansan vastauksen Herralle.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 Niin Herra sanoi Moosekselle: "Katso, minä tulen sinun tykösi paksussa pilvessä, että kansa kuulisi, kun minä puhun sinun kanssasi, ja uskoisi myös sinua ainiaan". Ja Mooses ilmoitti Herralle kansan vastauksen.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 Niin Herra sanoi Moosekselle: "Mene kansan luo ja pyhitä heidät tänä päivänä ja huomenna, ja peskööt he vaatteensa.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 Ja olkoot valmiit kolmanneksi päiväksi; sillä kolmantena päivänä Herra astuu koko kansan nähden alas Siinain vuorelle.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 Ja merkitse raja kansalle yltympäri ja sano: 'Varokaa nousemasta vuorelle tahi koskettamasta sen juureen. Jokainen, joka vuoreen koskee, rangaistakoon kuolemalla.
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 Älköön kenenkään käsi häneen koskeko, vaan hänet kivitettäköön tahi ammuttakoon kuoliaaksi. Olipa eläin tai ihminen, ei se saa jäädä eloon.' Vasta kun pitkä torven puhallus kuuluu, he nouskoot vuorelle."
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 Ja Mooses astui alas vuorelta kansan luo; ja hän pyhitti kansan, ja he pesivät vaatteensa.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 Ja hän sanoi kansalle: "Olkaa kolmanneksi päiväksi valmiit; älköön kukaan ryhtykö naiseen".
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 Ja kolmantena päivänä, kun aamu oli tullut, alkoi jylistä ja salamoida, ja paksu pilvi laskeutui vuoren ylle, ja kuului ylen kova pasunan ääni, niin että koko kansa, joka oli leirissä, vapisi pelosta.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 Silloin Mooses vei kansan leiristä Jumalaa vastaan, ja he asettuivat vuoren juurelle.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 Ja koko Siinain vuori peittyi savuun, kun Herra astui sille alas tulessa, ja siitä nousi savu niinkuin pätsin savu, ja koko vuori vapisi kovasti.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 Ja pasunan ääni koveni kovenemistaan. Mooses puhui, ja Jumala vastasi hänelle jylinällä.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 Ja Herra astui alas Siinain vuorelle, vuoren kukkulalle, ja Herra kutsui Mooseksen vuoren kukkulalle; ja Mooses nousi sinne ylös.
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 Niin Herra sanoi Moosekselle: "Astu alas ja varoita kansaa tunkeutumasta lähelle Herraa, häntä nähdäkseen, sillä silloin heistä monta kaatuu.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 Papitkin, jotka saavat lähestyä Herraa, pyhittäkööt itsensä, ettei Herra heitä tuhoaisi."
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 Mutta Mooses vastasi Herralle: "Kansa ei voi nousta Siinain vuorelle, sillä sinä olet varoittanut meitä ja sanonut: 'Merkitse raja vuoren ympäri ja pyhitä se'."
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 Niin Herra sanoi hänelle: "Astu alas ja tule taas ylös, sinä ja Aaron sinun kanssasi. Mutta papit ja kansa älkööt tunkeutuko ylös, Herraa lähelle, ettei hän heitä tuhoaisi."
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 Ja Mooses astui alas kansan luo ja sanoi heille tämän.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.

< 2 Mooseksen 19 >