< Psalmien 29 >
1 Davidin Psalmi. Tuokaat Herralle, te väkevät, tuokaat Herralle kunnia ja väkevyys.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Tuokaat Herralle hänen nimensä kunnia: kumartakaat Herraa pyhässä kaunistuksessa.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 Herran ääni käy vetten päällä: kunnian Jumala pauhaa, suurten vetten päällä.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 Herran ääni käy voimassa: Herran ääni käy suuressa kunniassa.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 Herran ääni särkee sedripuut, ja Herra särkee sedripuut Libanonissa.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 Hän hyppäyttää heitä niinkuin vasikan, sekä Libanonin että Sirionin, niinkuin nuoren yksisarvisen.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 Herran ääni leikkaa niinkuin tulen liekki.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 Herran ääni häälyttää korven, ja Herra liikuttaa Kadeksen korven.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 Herran ääni saattaa peurat poikimaan, ja paljastaa metsät: ja hänen templissänsä pitää koko hänen joukkonsa sanoman hänelle kunnian.
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Herra istuu vedenpaisumisen päällä: Herra pysyy Kuninkaana ijankaikkisesti.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Herra antaa kansallensa väkevyyden: Herra siunaa kansaansa rauhalla.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.