< Aamoksen 3 >

1 Kuulkaat tätä sanaa, jonka Herra puhuu teistä, te Israelin lapset, kaikista sukukunnista, jotka minä olen vienyt ulos Egyptin maalta, ja sanoin:
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 Kaikista sukukunnista maan päällä olen minä teidät ainoastaan korjannut; sen tähden tahdon minä myös teitä etsiä kaikissa teidän pahoissa töissänne.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Taitaako kaksi yhdessä vaeltaa, ellei he yhteen sovi?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Kiljuuko jalopeura metsässä, jos ei hänellä ruokaa ole? Parkuuko jalopeuran penikka luolastansa, ellei hän jotakin saanut ole?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Menneekö lintu paulaan maan päällä, kussa ei pyytäjää ole? Ottaneeko hän paulansa maasta, joka ei mitään vielä saanut ole?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Soitetaanko vaskitorvea kaupungissa, ja ei kansa hämmästy? Onko myös jotain pahaa kaupungissa, jota ei Herra tee?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Sillä ei Herra, Herra tee mitään, ellei hän ilmoita salauttansa palvelioillensa prophetaille.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 Jalopeura kiljuu, kuka ei pelkää? Herra, Herra puhuu, kuka ei ennusta?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Julistakaat Asdodin huoneissa ja Egyptin maan huoneissa, ja sanokaat: kootkaat teitänne Samarian vuorille, ja katsokaat, kuinka suuri vääryys ja väkivalta siellä on.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 Ei he taida oikeutta tehdä, sanoo Herra; vaan kokoovat tavaroita huoneissansa väkivallalla ja ryöstämisellä.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 Sentähden näin sanoo Herra, Herra: tämä maa piiritetään; ja sinä paiskataan alas sinun vallastas, ja sinun huonees raadellaan.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Näin sanoo Herra: Niinkuin paimen tempaa ulos jalopeuran suusta kaksi reittä eli korvan kappaleen; niin myös Israelin lapset pitää temmatuksi tuleman, jotka Samariassa asuvat, vuoteen loukkaassa ja kehdon kulmassa.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Kuulkaat ja todistakaat Jakobin huoneessa, sanoo Herra, Herra Jumala Zebaot.
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Sillä silloin, kuin minä Israelin synnit etsin, tahdon minä myös Betelin alttarin etsiä; ja alttarin sarvet pitää hakattaman pois, ja ne lankeeman maahan.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Ja tahdon talvihuoneen ja suvihuoneen maahan lyödä; ja elephantin luiset huoneet pitää hukkuman, ja paljo huoneita pitää häviämän, sanoo Herra.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Aamoksen 3 >