< 2 Timoteukselle 2 >

1 Vahvista siis sinus, minun poikani, sen armon kautta, joka Jesuksessa Kristuksessa on.
Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
2 Ja mitä sinä olet minulta monen todistajan kautta kuullut, niin käske uskollisille ihmisille, jotka myös muita olisivat soveliaat opettamaan.
Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
3 Kärsi vaivaa niinkuin luja Jesuksen Kristuksen sotamies.
Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
4 Ei yksikään sotamies sekoita itsiänsä elatuksen menoihin, sille kelvataksensa, joka hänen sotaan ottanut on.
Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
5 Ja jos joku kilvoittelee, niin ei hän kruunata, ellei hän toimellisesti kilvoittele.
Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
6 Peltomiehen, joka pellon rakentaa, pitää ensin hedelmästä nautitseman.
Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
7 Ymmärrä, mitä minä sanon: Herra antakoon sinulle ymmärryksen kaikissa;
Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
8 Muista Jesuksen Kristuksen päälle, joka kuolleista noussut on: Davidin siemenestä minun evankeliumini jälkeen,
Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
9 Jossa minä vaivaa kärsin kahleisiin asti niinkuin pahantekiä; vaan ei Jumalan sana ole sidottu.
wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
10 Sentähden minä kärsin kaikki valittuin tähden, että hekin saisivat Jesuksessa Kristuksessa autuuden, ijankaikkisen kunnian kanssa. (aiōnios g166)
Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios g166)
11 Se on totinen sana: jos me ynnä olemme kuolleet, niin me myös ynnä elämme;
Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
12 Jos me kärsimme, niin me myös ynnä hallitsemme; jos me hänen kiellämme, niin hän meidätkin kieltää;
in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
13 Ellemme usko, niin hän pysyy kuitenkin uskollisena, joka ei itsiänsä kieltää taida.
in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
14 Näitä neuvo ja todista Herran edessä, ettei he sanoista riitelisi, joka ei mihinkään kelpaa, vaan ainoastaan luovuttamaan niitä jotka kuulevat.
Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
15 Pyydä itses Jumalalle osoittaa toimelliseksi ja laittamattomaksi työntekijäksi, joka oikein totuuden sanan jakaa.
Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
16 Mutta siivottomat ja kelvottomat sanat hylkää, jotka paljon jumalatointa menoa saattavat.
Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
17 Ja heidän puheensa syö ympäriltänsä niinkuin ruumiin mato; joista on Hymeneus ja Philetus,
Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
18 Jotka totuudesta ovat erehtyneet, sanoen ylösnousemisen jo tapahtuneen, ja ovat muutamat uskosta kääntäneet.
waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
19 Mutta Jumalan vahva perustus kuitenkin pysyy, joka tällä kiinnitetty on: Herra tuntee omansa: ja lakatkaan jokainen vääryydestä, joka Kristuksen nimeä mainitsee.
Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
20 Mutta suuressa huoneessa ei ole ainoastaan kultaiset ja hopiaiset astiat, vaan myös puiset ja saviset, ja muutamat tosin kunniaksi, mutta muutamat häpiäksi.
A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
21 Jos joku itsensä senkaltaisista ihmisistä puhdistaa, se tulee kunniaan pyhitetyksi astiaksi, perheenisännälle tarpeelliseksi ja kaikkiin hyviin töihin valmistetuksi.
In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
22 Nuoruuden himot vältä; mutta noudata vanhurskautta, uskoa, rakkautta ja rauhaa kaikkein niiden kanssa, jotka puhtaasta sydämestä Herraa rukoilevat.
Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
23 Hullut ja turhat kysymykset hylkää, tietäen, että ne ainoastaan riidat synnyttävät.
Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
24 Mutta ei Herran palvelian tule riitaisen olla, vaan siviän jokaista kohtaan, opettavaisen, pahoja kärsiväisen.
Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
25 Hiljaisuudessa nuhtelevaisen vastahakoisia; jos Jumala heille joskus antais parannuksen totuutta ymmärtämään,
Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
26 Ja he jälleen katuisivat ja perkeleen paulasta pääsisivät, jolta he hänen tahtonsa jälkeen vangitut ovat.
su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.

< 2 Timoteukselle 2 >