< Matteus 9 >
1 Nõnda läks siis Jeesus paadiga tagasi üle järve linna, kus ta elas.
Yesu ya shiga jirgin ruwa, ya ƙetare ya zo garinsa.
2 Seal toodi tema juurde matil lamav halvatud mees. Kui Jeesus nägi nende usku, ütles ta halvatule: „Mu sõber, ära kurvasta! Sinu patud on andeks antud.“
Waɗansu mutane suka kawo masa wani shanyayye, kwance a tabarma. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Kada ka damu saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
3 Selle peale ütlesid mõned vaimulikud õpetajad isekeskis: „Ta teotab Jumalat!“
Da jin wannan, waɗansu malaman dokoki suka ce wa juna, “Wannan mutum yana yin saɓo!”
4 Kuid Jeesus teadis, mida nad mõtlevad. Ta küsis neilt: „Miks te mõtlete kurje mõtteid?
Sane da tunaninsu, Yesu ya ce, “Me ya sa kuke da mugun tunani a zuciyarku?
5 Mida on kergem öelda: „Su patud on andeks antud“või „Tõuse üles ja kõnni“?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuwa a ce, ‘Tashi ka yi tafiya?’
6 Aga et veenda teid, et inimese Pojal on õigus patte andeks anda …“Ta ütles halvatule: „Tõuse üles, võta oma matt ja mine koju!“
Amma don ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
7 Mees tõusis üles ja läks koju.
Mutumin kuwa ya tashi ya tafi gida.
8 Kui rahvahulgad nägid, mis oli juhtunud, olid nad ehmunud. Siis ülistasid nad Jumalat, et ta oli andnud inimesele sellise väe.
Da taron suka ga haka, sai suka cika da tsoro, suka yabi Allah wanda ya ba wa mutane irin ikon nan.
9 Kui Jeesus sealt edasi läks, nägi ta maksukogumispunktis istumas meest nimega Matteus. Jeesus kutsus teda: „Järgi mind!“Ta tõusis üles ja järgnes Jeesusele.
Da Yesu ya yi gaba daga wurin, sai ya ga wani mutum mai suna Mattiyu zaune a inda ake karɓar haraji. Ya ce masa, “Bi ni.” Mattiyu kuwa ya tashi ya bi shi.
10 Sel ajal kui Jeesus sõi Matteuse kodus, tuli palju maksukogujaid ja patuseid ning nad istusid lauas koos Jeesuse ja tema jüngritega.
Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Mattiyu, masu karɓar haraji da yawa da kuma masu zunubi suka zo suka kuwa ci tare da shi da kuma almajiransa.
11 Kui variserid seda nägid, küsisid nad Jeesuse jüngritelt: „Miks teie Õpetaja sööb koos maksukogujate ja patustega?“
Sa’ad da Farisiyawa suka ga haka, sai suka tambayi almajiransa suka ce, “Don me malaminku yake ci tare da masu karɓar haraji, da masu zunubi?”
12 Kui Jeesus seda küsimust kuulis, vastas ta: „Arsti ei vaja terved, vaid haiged.
Da jin wannan, Yesu ya ce, “Ai, ba masu lafiya ba ne su bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
13 Minge ja uurige välja, mida see tähendab: „Ma tahan halastust, mitte ohvrit. Sest ma ei tulnud kutsuma neid, kes teevad seda, mis on õige; ma tulin kutsuma patuseid.““
Amma ku je ku koyi abin da wannan yake nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba.’Gama ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
14 Siis tulid Johannese jüngrid ja küsisid: „Miks on nii, et meie ja variserid paastume sageli, aga sinu jüngrid ei paastu?“
Sai almajiran Yohanna suka zo suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa mu da Farisiyawa muke azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
15 „Kas pulmakülalised kurvastavad, kui peigmees on nende juures?“vastas Jeesus. „Aga tuleb aeg, mil peigmees võetakse nende juurest ära, ja siis nad paastuvad.
Yesu ya amsa ya ce, “Yaya baƙin ango za su yi makoki yayinda yake tare da su? Lokaci yana zuwa da za a ɗauke ango daga gare su, sa’an nan za su yi azumi.
16 Keegi ei pane vanadele rõivastele uut riiet paigaks, muidu tõmbab see kokku ja rebend läheb hullemaks.
“Ba mai yin faci da sabon ƙyalle a kan tsohuwar riga, gama facin zai kece rigar yă sa kecewar ma ta fi ta dā muni.
17 Keegi ei pane uut veini vanadesse lähkritesse, muidu lähkrid rebenevad, vein voolab maha ja lähkrid on rikutud. Ei, uus vein pannakse uutesse nahklähkritesse ja mõlemad kestavad.“
Mutane kuma ba sa zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In suka yi haka, salkunan za su farfashe, ruwan inabin kuwa yă zube salkunan kuma su lalace. A’a, ai, sukan zuba sabon ruwan inabi ne a cikin sababbin salkuna, don a kiyaye dukan biyun.”
18 Sel ajal kui ta neile seda rääkis, tuli üks ülematest ja kummardus tema ees. „Mu tütar suri just, “ütles mees Jeesusele. „Aga ma tean, et kui sa tuled ja paned oma käe tema peale, siis ta tuleb ellu tagasi.“
Yayinda yake faɗin wannan, sai wani mai mulki ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Yanzu-yanzu diyata ta rasu. Amma ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, za tă kuwa rayu.”
19 Jeesus ja tema jüngrid tõusid ja läksid tema järel.
Yesu ya tashi ya tafi tare da shi, haka ma almajiransa.
20 Sel hetkel tuli tema taha üks naine, kes oli kaksteist aastat veritsustõves olnud, ja puudutas tema kuube.
A daidai wannan lokaci sai ga wata mace wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini ta raɓo ta bayansa ta taɓa gefen rigarsa.
21 Ta ütles endamisi: „Kui ma vaid saaksin puudutada tema kuube, siis ma saaksin terveks.“
Ta ce a ranta, “Ko da rigarsa ce kawai na taɓo, zan warke.”
22 Jeesus pöördus ja vaatas talle otsa. „Ole rõõmus, sest sinu usk minusse on su terveks teinud, “ütles ta naisele. Naine sai otsekohe terveks.
Yesu ya juya ya gan ta. Sai ya ce, “Kada ki damu diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke.” Nan take macen ta warke.
23 Jeesus jõudis ametniku koju. Ta nägi flöödimängijaid ja rahvahulka, mis nuttis valjusti.
Da Yesu ya shiga gidan mai mulkin ya ga masu busan sarewa da taro mai hayaniya,
24 „Palun minge ära, “ütles ta rahvale, „sest tüdruk ei ole surnud, ta vaid magab.“Aga nad naersid ja heitsid tema üle nalja.
sai ya ce, “Ku ba da wuri. Ai, yarinyar ba tă mutu ba, tana barci ne.” Amma suka yi masa dariya.
25 Kuid kui rahvas oli laiali saadetud, läks Jeesus sisse, võttis tüdrukul käest kinni ja tüdruk tõusis üles.
Bayan an fitar da taron waje, sai ya shiga ciki ya kama yarinyar a hannu, ta kuwa tashi.
26 Sõnum juhtunust levis üle kogu selle piirkonna.
Labarin wannan kuwa ya bazu ko’ina a yankin.
27 Kui Jeesus sealt edasi läks, järgnesid talle kaks pimedat meest, kes hüüdsid: „Taaveti Poeg, palun halasta meie peale!“
Da Yesu ya fita daga can, sai waɗansu makafi biyu suka bi shi, suna kira, suna cewa, “Ka yi mana jinƙai, Ɗan Dawuda!”
28 Kui Jeesus jõudis majja, kus ta peatus, tulid ka pimedad mehed sisse. „Kas te olete veendunud, et ma olen võimeline seda tegema?“küsis ta neilt. „Jah, Issand, “vastasid nad.
Da ya shiga cikin gida, sai makafin nan suka zo wurinsa, ya kuma tambaye su, “Kun gaskata cewa ina iya yin wannan?” Suka amsa suka ce, “I, Ubangiji.”
29 Siis Jeesus puudutas nende silmi ja ütles: „See toimub, sest te usute minusse!“
Sa’an nan ya taɓa idanunsu ya ce, “Bisa ga bangaskiyarku a yi muku haka”;
30 Ja nad nägid jälle. Siis Jeesus hoiatas neid: „Vaadake, et keegi sellest teada ei saaks.“
sai idanunsu suka buɗe. Yesu ya gargaɗe su sosai ya ce, “Ku lura kada wani yă san wani abu game da wannan.”
31 Aga nad läksid ja rääkisid Jeesusest kõikjal.
Amma suka fita suka yi ta baza labari game da shi ko’ina a wannan yankin.
32 Kui Jeesus ja tema jüngrid olid lahkumas, toodi tema juurde mees, kes oli tumm ja kurjast vaimust vaevatud.
Yayinda suke fitowa, sai aka kawo wa Yesu wani mutum mai aljani, da ba ya iya magana.
33 Kui kuri vaim oli temast välja aetud, siis tumm mees rääkis, ja rahvahulk oli hämmastuses. „Midagi seesugust pole varem Iisraelis juhtunud, “ütlesid nad.
Sa’ad da aka fitar da aljanin kuwa, sai beben ya yi magana. Taron suka yi mamaki suka ce, “Ba a taɓa ganin irin wannan abu a Isra’ila ba.”
34 Aga variserid täheldasid: „Ta ajab kurje vaime välja kurjade vaimude ülema väe abil.“
Amma Farisiyawa suka ce, “Ai, da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
35 Jeesus käis igal pool ning külastas linnu ja külasid. Ta õpetas nende sünagoogides, rääkis head sõnumit kuningriigist ning tervendas igasuguseid haigusi ja vaevusi.
Yesu ya zazzaga dukan garuruwa da ƙauyuka, yana koyarwa a majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin yana kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
36 Kui Jeesus nägi rahvahulki, oli ta sügavalt liigutatud kaastundest nende vastu, sest nad olid mures ja abitud, nagu lambad ilma karjaseta.
Da ya ga taron mutane, sai ya ji tausayinsu, domin an wulaƙanta su ba su kuma da mai taimako, kamar tumaki marasa makiyayi.
37 Ta ütles oma jüngritele: „Lõikus on suur, kuid töötegijaid on vähe.
Sai ya ce wa almajiransa, “Girbi yana da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne.
38 Palvetage lõikuse Issanda poole ja paluge tal saata veel töötegijaid oma lõikust koguma.“
Saboda haka ku roƙi Ubangijin girbi, yă aiko da ma’aikata cikin gonarsa na girbi.”