< Matteus 5 >
1 Kui Jeesus nägi rahvahulki enda järel käimas, läks ta üles mäele. Seal istus ta koos oma jüngritega maha.
Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa,
2 Ta hakkas neid õpetama ning ütles:
sai ya fara koya musu. Yana cewa,
3 „Õnnistatud on need, kes tunnevad ära, et nad on vaimulikult vaesed, sest nende päralt on taevariik.
“Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu, gama mulkin sama nasu ne.
4 Õnnistatud on need, kes kurvastavad, sest neid lohutatakse.
Masu albarka ne waɗanda suke makoki, gama za a yi musu ta’aziyya.
5 Õnnistatud on need, kes on heatahtlikud, sest nende päralt on kogu maailm.
Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u, gama za su gāji duniya.
6 Õnnistatud on need, kelle suurim soov on teha seda, mis on õige, sest nende soov täidetakse.
Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci, gama za a ƙosar da su.
7 Õnnistatud on need, kes on halastavad, sest nende suhtes ilmutatakse halastust.
Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai, gama za a nuna musu jinƙai.
8 Õnnistatud on need, kel on puhas süda, sest nemad näevad Jumalat.
Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya, gama za su ga Allah.
9 Õnnistatud on need, kes näevad vaeva rahu loomisel, sest neid hüütakse Jumala lasteks.
Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci, gama za a kira su’ya’yan Allah.
10 Õnnistatud on need, keda kiusatakse taga sellepärast, mis on õige, sest nende päralt on taevariik.
Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci, gama mulkin sama nasu ne.
11 Õnnistatud olete teie, kui inimesed teid solvavad ja taga kiusavad ning süüdistavad teid minu pärast igasugustes halbades asjades.
“Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni.
12 Olge rõõmsad, olge tõesti rõõmsad, sest te saate suure tasu taevas, sest samamoodi kiusasid nad taga prohveteid, kes olid enne teid.
Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.
13 Teie olete maa sool, aga kui sool muutub maitsetuks, kuidas saab selle jälle soolaseks teha? Sellest pole kasu millegi jaoks, nii et see visatakse välja jalgade alla tallamiseks.
“Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.
14 Teie olete maailma valgus. Mäe otsa ehitatud linn ei saa varjule jääda.
“Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa.
15 Keegi ei süüta lampi ega pane seda ämbri alla. Ei, see asetatakse lambijalale ning see valgustab kõiki majas.
Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida.
16 Samamoodi peate ka teie laskma oma valgusel paista kõigi ees, et nad näeksid häid asju, mida te teete, ning ülistaksid teie taevast Isa.
Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.
17 Ärge arvake, et ma tulin seadust või prohvetite kirju tühistama. Ma ei tulnud neid tühistama, vaid täitma.
“Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su.
18 Ma kinnitan teile, kuni taevas ja maa püsivad, ei kao seadusest ainsat tähte ega märki enne, kui kõik on täitunud.
Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome.
19 Seega, kes iganes põlgab kas või kõige tähtsusetumat käsku ja õpetab nii inimesi, seda nimetatakse taevariigis kõige tähtsusetumaks; aga kes iganes järgib ja õpetab käske, seda nimetatakse taevariigis suureks.
Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama.
20 Ma ütlen teile, kui teie moraalne õigsusei ole rohkem kui vaimulike õpetajate ja variseride oma, ei saa te kunagi taevariiki.
Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.
21 Te olete kuulnud, et seadus ütles inimestele muiste: „Sa ei tohi tappa, ja igaüks, kes tapab, mõistetakse süüdi.“.
“Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai; kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’
22 Aga mina ütlen teile, igaüks, kes on oma venna peale vihane, mõistetakse süüdi. Kes iganes nimetab oma venda idioodiks, peab vastust andma nõukogu ees, aga kes iganes teisi sõimab, läheb kohtutulle. (Geenna )
Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta. (Geenna )
23 Kui sa oled altari juures ohvrit toomas ja sulle meenub, et su vennal on midagi sinu vastu,
“Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci,
24 siis jäta oma ohver altarile ja tee esmalt temaga rahu ning alles pärast tule tagasi ja too oma ohver.
sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.
25 Kui sa oled oma vastasega teel kohtusse, siis püüa asjad kiiresti lahendada. Muidu võib su vastane anda sind kohtuniku kätte ja kohtunik annab sind kohtu ametniku kätte ning sind heidetakse vanglasse.
“Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku.
26 Ma räägin teile tõtt: sa ei pääse sealt välja enne, kui oled ära maksnud oma viimasegi penni.
Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.
27 Te olete kuulnud, et seadus ütles: „Ära riku abielu.“
“Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’
28 Aga mina ütlen teile, et igaüks, kes vaatab naist himuralt, on temaga mõttes juba abielu rikkunud.
Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa.
29 Kui su parem silm juhib sind patustama, siis kisu see välja ja viska minema, sest parem on kaotada üks osa oma kehast, kui et kogu su keha visatakse kohtutulle. (Geenna )
In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
30 Kui su parem käsi juhib sind patustama, siis lõika see maha ja viska minema, sest sul on parem kaotada üks jäsemetest, kui et kogu su keha visatakse kohtutulle. (Geenna )
In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. (Geenna )
31 Seadus ütles ka: „Kui mees lahutab oma naisest, peab ta andma naisele lahutustunnistuse.“
“An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’
32 Aga mina ütlen teile, et iga mees, kes lahutab oma naisest muidu kui seksuaalse ebamoraalsuse tõttu, sunnib naist abielu rikkuma, ja kes iganes abiellub lahutatud naisega, rikub abielu.
Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.
33 Ja veel, te olete kuulnud, et seadus ütles inimestele ammu: „Sa ei tohi valet vanduda. Hoolitse selle eest, et pead oma vandeid, mille Issandale annad.“
“Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’
34 Aga mina ütlen teile: ärge üldse vanduge. Ärge vanduge taeva juures, sest see on Jumala troon.
Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne;
35 Ärge vanduge maa juurest, sest see on Jumala jalajäri. Ärge vanduge Jeruusalemma juures, sest see on suure Kuninga linn.
ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne.
36 Ärge vanduge isegi oma pea juures, sest te ei suuda üht juuksekarvagi valgeks või mustaks teha.
Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba.
37 Öelge lihtsalt jah või ei – mis on üle selle, on kurjast.
Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.
38 Te olete kuulnud, et seadus ütleb: „Silm silma vastu ja hammas hamba vastu.“
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’
39 Aga mina ütlen teile, ära hakka vastu sellele, kes on kuri. Kui keegi lööb sind parema põse pihta, pööra talle ka teine põsk.
Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma.
40 Kui keegi tahab sind kohtusse kaevata ja võtab su särgi, anna talle ka oma kuub.
In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma.
41 Kui keegi nõuab, et kõnniksid ühe miili, mine temaga kaks miili.
In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu.
42 Anna sellele, kes sinult palub, ja ära pöördu ära sellest, kes tahab sinult laenata.
Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.
43 Te olete kuulnud, et seadus ütleb: „Armasta oma ligimest ja vihka oma vaenlast.“
“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka, ka kuma ƙi abokin gābanka.’
44 Aga mina ütlen teile, armastage oma vaenlasi ja palvetage nende eest, kes teid taga kiusavad,
Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābankukuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a,
45 et te võiksite saada oma taevase Isa lasteks. Sest tema päike paistab nii heade kui halbade peale ning ta laseb vihma sadada nii nende peale, kes toimivad õigesti, kui ka nende peale, kes toimivad valesti.
don ku zama’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci.
46 Sest kui sa armastad ainult neid, kes sind armastavad, mis tasu sa saad? Kas mitte isegi maksukogujad ei tee seda?
In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba?
47 Kui sa kõneled lahkelt ainult oma pereliikmetega, mida enamat sa siis teed kui keegi teine? Isegi paganad teevad seda!
In kuwa kuna gai da’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba?
48 Kasva suureks ja saa täielikult usaldusväärseks, just nagu teie taevane Isa on usaldusväärne.“
Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.