< Luuka 8 >
1 Varsti pärast seda käis Jeesus ringi linnades ja külades ning kuulutas head sõnumit Jumala riigist. Kaksteist jüngrit käisid koos temaga,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 peale selle hulga naisi, kelle ta oli kurjadest vaimudest ja haigustest terveks teinud: Maarja, keda hüütakse Magdaleenaks, kellest ta oli seitse kurja vaimu välja ajanud;
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Johanna, Heroodese kojaülema Kuusase naine; Susanna ja veel paljud teised, kes teda oma isiklike vahenditega toetasid.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Kord, kui oli kogunenud suur hulk inimesi, kes olid tulnud paljudest linnadest teda vaatama, hakkas Jeesus neile kõnelema ja kasutas näitlikustamiseks jutustust.
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 „Üks põllumees läks välja külvama. Kui ta seemet laiali puistas, kukkus osa sellest tee peale, kus inimesed selle jalgade alla trampisid ja linnud ära sõid.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Osa seemnest kukkus kivisele pinnale ja kui seeme oli idanenud, närbusid võrsed niiskuse puudumise tõttu.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Osa seemneid kukkus ohakate sekka ja kui mõlemad kasvasid, lämmatasid ohakad vilja ära.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Osa seemnest kukkus hea maa peale ning andis hiljem saaki sada korda rohkem sellest, mis oli külvatud.“Kui ta oli seda rääkinud, hüüdis ta: „Kui teil on kõrvad, siis kuulake!“
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Aga tema jüngrid küsisid talt: „Mida see mõistujutt tähendab?“
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Jeesus vastas: „Teile on antud võimalus heita pilk Jumala riigi saladustesse, kuid ülejäänutele on antud mõistujutud, et „isegi kui nad näevad, siis nad tegelikult ei näe, ja kuigi nad kuulevad, ei saa nad tegelikult aru.“
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Selle mõistujutu tähendus on järgmine: seeme on Jumala sõna.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Seemned, mis kukuvad tee peale, on need, kes kuulevad sõnumit, kuid kurat tuleb ja näppab tõe nende mõistusest ära, nii et nad ei usu Jumalasse ega saa päästetud.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Seemned, mis kukuvad kivisele pinnale, on need, kes kuulevad sõnumit ja võtavad selle rõõmuga vastu, kuid neil ei ole juuri. Mõnda aega nad usuvad, aga kui tulevad rasked ajad, annavad nad alla.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Seemned, mis kukuvad ohakate sekka, on need, kes kuulevad sõnumit, kuid selle elu asjad − mured, rikkus, lõbud − lämmatavad selle, nii et nad ei kanna vilja.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Heasse mulda külvatud seemned on need, kes on siirad ja teevad seda, mis on õige. Nad kuulevad tõesõnumit, haaravad sellest kinni ning annavad püsivuse tõttu head saaki.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Ei süüdata lampi, et seda siis ämbriga katta või voodi alla peita. Ei, lamp asetatakse lambijalale, et kõik, kes sisse tulevad, näeksid selle valgust.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Sest ei ole midagi varjatut, mis ei saaks avalikuks; ei ole midagi salajast, mis ei saaks teatavaks ja selgeks.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Nii et pange tähele, kuidas te kuulete. Neile, kes on vastu võtnud, antakse juurde; neilt, kes vastu ei võta, võetakse ära isegi see, mis neil enda arvates on!“
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Siis jõudsid kohale Jeesuse ema ja vennad, kuid nad ei pääsenud läbi rahvahulga tema juurde.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Jeesusele öeldi: „Su ema ja vennad on väljas. Nad tahavad sind näha.“
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 „Mu ema ja vennad on need, kes kuulevad Jumala sõna ja teevad, mida see käsib, “vastas Jeesus.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Ühel päeval ütles Jeesus oma jüngritele: „Lähme üle järve teisele kaldale.“Nii astusid nad paati ja asusid teele.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Kui nad seilasid, jäi Jeesus magama ja alla järvele tuli torm. Paat hakkas veega täituma ja oli oht põhja minna.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Nad läksid Jeesuse juurde ja äratasid ta üles „Õpetaja, õpetaja, me upume!“ütlesid nad. Jeesus ärkas üles ning käskis tuulel ja tormistel lainetel vaikida. Nii juhtuski ja kõik oli rahulik.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 „Kus on teie usk?“küsis ta neilt. Kohkunult ja hämmastunult ütlesid nad üksteisele: „Kes see siis on? Ta käsib tuuli ja vett ja need kuuletuvad talle!“
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Nad seilasid üle järve gerasalaste territooriumile, mis asub Galilea vastaskaldal.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Kui Jeesus astus paadist välja kaldale, tuli talle linnast vastu kurjast vaimust vaevatud mees. Pikka aega ei olnud ta riideid kandnud ega majas elanud. Ta elas hauakambrites.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Kui ta Jeesust nägi, hakkas ta karjuma, langes Jeesuse jalge ette maha ja küsis valju häälega: „Mida sa minust tahad, Jeesus, Kõigekõrgema Jumala Poeg? Ära piina mind, ma anun sind!“
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Sest Jeesus oli juba käskinud kurjal vaimul mehest lahkuda. See oli sageli teda oma valdusesse võtnud ning hoolimata sellest, et teda oli kettide ja vangiraudadega kinni pandud, lõhkus ta ketid ning kuri vaim oli teda kõrbesse kihutanud.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 „Mis su nimi on?“küsis Jeesus talt. „Leegion, “vastas ta, sest temasse oli sisenenud palju kurje vaime.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Nad palusid, et Jeesus ei käsiks neil minna tühjusesse. (Abyssos )
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos )
32 Lähedal asuval mäenõlval oli söömas suur seakari ja kurjad vaimud anusid teda, et ta lubaks neil sigadesse minna. Jeesus andis neile loa,
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 seega lahkusid kurjad vaimud mehest ja sisenesid sigadesse. Kari tormas järsku nõlva pidi alla järve ja uppus.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Kui seakarjused nägid, mis juhtus, jooksid nad minema ning kuulutasid seda linnas ja maal.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Rahvas läks välja vaatama, mis oli juhtunud. Kui nad tulid Jeesuse juurde, leidsid nad mehe, kes oli kurjadest vaimudest vabastatud. Ta istus Jeesuse jalgade juures, kandis riideid ja oli terve mõistuse juures. Rahvas hakkas kartma.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Need, kes olid juhtunut näinud, selgitasid, kuidas kurjadest vaimudest vaevatud mees oli terveks saanud.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Siis kõik Gerasa ümbruskonna rahvas palus Jeesusel lahkuda, sest neid valdas hirm. Nii astus ta paati ja läks tagasi.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Mees, kes oli deemonitest vabaks saanud, palus, et ta võiks kaasa minna, kuid Jeesus saatis ta minema.
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 „Mine koju tagasi ja räägi inimestele kõigest, mida Jumal on sinu heaks teinud, “käskis Jeesus. Nõnda siis mees läks ja kõneles kogu linnas kõigest, mida Jeesus oli tema heaks teinud.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Kui Jeesus tagasi tuli, oli kogunenud teda vastu võtma rahvahulk, kes teda innukalt ootas.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Üks neist oli mees nimega Jairus, sünagoogi ülem, kes tuli ja langes Jeesuse jalge ette. Ta anus, et Jeesus tuleks tema koju,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 sest tema ainus tütar oli suremas. Ta oli umbes kaheteistkümneaastane. Sel ajal kui Jeesus oli teel sinna, tungles tema ümber rahvahulk.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Rahva seas oli üks naine, kes oli kaksteist aastat veritsemise all kannatanud. Ta oli kulutanud kogu oma vara arstide peale, kuid keegi neist ei olnud suutnud teda aidata.
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 Ta lähenes Jeesusele selja tagant ja puudutas tema rüüd. Kohe lõppes veritsemine.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 „Kes mind puudutas?“küsis Jeesus. Kõik ümberolijad eitasid puudutamist. „Aga, õpetaja, “ütles Peetrus, „sinu ümber tungleb rahvas ja nad müksavad sind kogu aeg.“
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 „Keegi puudutas mind, “vastas Jeesus. „Ma tean, sest vägi läks minust välja.“
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Kui naine mõistis, et ta ei saa märkamatuks jääda, astus ta värisedes esile ja langes Jeesuse jalge ette maha. Seal kõigi ees selgitas ta põhjust, miks ta oli Jeesust puudutanud, ja et ta oli silmapilkselt terveks saanud.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Jeesus lausus talle: „Tütar, su usk on su terveks teinud, mine rahus.“
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Sel ajal kui ta alles rääkis, tuli keegi sünagoogi ülema kodust, et talle öelda: „Sinu tütar on surnud. Sul pole vaja enam Õpetajat tülitada.“
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Aga kui Jeesus seda kuulis, ütles ta Jairusele: „Ära karda. Kui sa usud, saab ta terveks.“
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Kui Jeesus maja juurde jõudis, ei lubanud ta sisse kedagi peale Peetruse, Johannese ja Jaakobuse ning tüdruku isa ja ema.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Seal nutsid ja leinasid kõik inimesed tüdruku pärast. „Ärge nutke, “ütles Jeesus neile. „Ta ei ole surnud, ta lihtsalt magab.“
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Nad naersid tema üle, sest nad teadsid, et tüdruk on surnud.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Kuid Jeesus võttis tüdrukul käest kinni ja ütles valju häälega: „Mu laps, tõuse üles!“
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Tüdruk ärkas ellu ja tõusis kohe püsti. Jeesus käskis neil talle midagi süüa anda.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Tüdruku vanemad olid toimunust jahmunud, kuid Jeesus ütles, et nad ei räägiks sellest kellelegi.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.