< Luuka 2 >
1 Sel ajal andis keiser Augustus välja seaduse, et Rooma impeeriumis tuleb kõiki hõlmav rahvaloendus.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 See oli esimene rahvaloendus Süüria maavalitseja Küreeniuse ajal.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 Niisiis läks igaüks oma linna end kirja panema.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 Joosep põlvnes kuningas Taavetist, seepärast lahkus ta Galileas asuvast Naatsaretist, et minna Juudamaale Petlemma, Taaveti linna.
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 Ta läks end sinna kirja panema koos Maarjaga, kes oli temaga kihlatud ja lapseootel.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 Kui nad seal olid, jõudis kätte lapsesaamise aeg.
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 Maarja tõi ilmale oma esmasündinud poja, mähkis ta riidelappidesse ja asetas sõime, sest võõrastemajas ei olnud vabu tube.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 Seal lähedal olid mõned karjased öösel väljadel ja valvasid oma karja.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 Neile ilmus Issanda ingel ja Issanda hiilgus paistis nende ümber. Nad kohkusid üliväga!
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 „Ärge kartke!“ütles ingel neile. „Tulin teile tooma head uudist, mis rõõmustab kõiki inimesi.
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 Täna sündis teile siin, Taaveti linnas, Päästja. Ta on Messias, Issand.
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 Te tunnete ta ära selle märgi järgi: te leiate lapse riidelappidesse mähitud ja sõimes lebamas.“
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 Äkki ilmus palju taevaseid olevusi, kes ülistasid Jumalat, öeldes:
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 „Au olgu taeva Jumalale ja maa peal rahu inimestele, kes on talle meele järele!“
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 Pärast seda kui inglid olid lahkunud ja tagasi taevasse läinud, ütlesid karjased üksteisele: „Lähme Petlemma ja vaatame, mis on toimunud sellega seoses, millest Issand meile rääkis.“
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 Nad kiirustasid sinna ning leidsid Maarja, Joosepi ja lapse, kes lamas sõimes.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 Kui nad olid seda ise näinud, siis levitasid nad uudist toimunust ja sellest, mida oli neile selle lapse kohta räägitud.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 Kõik, kes seda kuulsid, olid karjaste jutust hämmastunud.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 Kuid Maarja pidas hoolikalt meeles kõik, mis oli juhtunud, ning mõtles selle peale sageli.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 Karjased läksid tagasi oma karja valvama ning ülistasid ja tänasid Jumalat kõige eest, mida nad olid kuulnud ja näinud, sest kõik oli just nii, nagu neile oli öeldud.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 Kaheksa päeva pärast oli aeg laps ümber lõigata ja talle pandi nimeks Jeesus. See oli nimi, mille ingel oli andnud enne, kui ema oli lapseootele jäänud.
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 Kui nende puhastusaeg vastavalt Moosese seadusele lõppes, viisid Joosep ja Maarja ta Jeruusalemma, et teda Issanda ette tuua,
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 nagu Issanda seadus ütleb: „Kõik esmasündinud pojad tuleb Issandale pühitseda.“
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 Seal tõid nad ohvri, nagu Jumala seadus määrab, „paari turteltuvisid või kaks noort tuvi“.
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 Tol ajal elas Jeruusalemmas mees nimega Siimeon. Siimeon tegi seda, mis oli hea, ja ta oli väga vaga. Ta ootas pikisilmi Iisraeli lootust ja Püha Vaim oli tema peal.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 Püha Vaim oli talle näidanud, et ta ei sure enne, kui on näinud Issanda Messiat.
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 Vaimu juhtimist järgides läks ta templisse. Kui Jeesuse vanemad tõid väikese poisi, et teda pühendada, nagu Seadus nõudis,
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 võttis Siimeon Jeesuse sülle, tänas Jumalat ja ütles:
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 „Issand ja Õpetaja, nüüd saad oma sulasel lasta rahus surra, nagu sa tõotasid,
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 sest ma olen ise näinud sinu päästet,
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 mille sa oled kõigi jaoks valmistanud.
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 Ta on valgus, mis näitab rahvastele sind, sinu rahva Iisraeli hiilgust.“
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 Jeesuse isa ja ema olid rabatud sellest, mida Siimeon tema kohta ütles.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 Seejärel Siimeon õnnistas neid ja ütles Jeesuse emale Maarjale: „Määratud on, et selle lapse tõttu paljud Iisraelis langevad ja paljud tõusevad. Ta on märk Jumalalt, mille paljud hülgavad,
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 näidates sellega, mida nad tegelikult mõtlevad. Aga sina tunned, nagu tungiks mõõk otse sinust läbi.“
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 Jeruusalemmas elas ka naisprohvet Hanna. Ta oli Aaseri suguharust, Penueli tütar, ning ta oli väga vana. Ta oli olnud abielus seitse aastat
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 ning oli siis leseks jäänud. Ta oli kaheksakümne nelja aastane. Ta veetis aega templis Jumalat ülistades, paastudes ja palvetades.
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 Just siis tuli ta nende juurde ja hakkas Jumalat kiitma. Ta kõneles Jeesusest kõigile, kes ootasid seda aega, mil Jumal Jeruusalemma vabastab.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 Kui nad olid täitnud kõik, mida Jumala seadus nõudis, läksid nad tagasi oma kodulinna Naatsaretti Galileas.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 Laps kasvas tugevaks ja oli väga arukas. Jumala õnnistus oli temaga.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 Jeesuse vanemad rändasid igal aastal paasapühaks Jeruusalemma.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 Kui Jeesus oli kaheteistkümneaastane, läksid nad pühadele nagu alati.
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 Kui pühad olid läbi ja oli aeg koju naasta, jäi poiss Jeesus Jeruusalemma, kuid tema vanemad ei teadnud seda.
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 Nad oletasid, et ta oli koos kõigi teistega koju rändamas. Kui päev oli möödunud, hakkasid nad teda sõprade ja sugulaste juurest otsima.
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 Kui nad ei suutnud teda leida, läksid nad tagasi Jeruusalemma, et teda seal otsida.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 Alles kolme päeva pärast leidsid nad ta templist. Ta istus vaimulike õpetajate keskel, kuulas neid ja esitas neile küsimusi.
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 Kõik, kes kuulsid teda rääkimas, olid tema arusaamisest ja vastustest üllatunud.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 Tema vanemad olid täiesti segaduses, kui nad nägid, mida ta teeb. Ema küsis talt: „Poeg, miks sa meiega niimoodi käitusid? Su isa ja mina oleme end haigeks muretsenud! Oleme sind igalt poolt otsinud!“
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 „Miks te mind otsisite?“vastas Jeesus. „Kas te ei teadnud, et ma peaksin olema siin, oma Isa kojas?“
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 Aga nad ei saanud aru, mida ta sellega mõtles.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 Siis läks ta koos nendega tagasi Naatsaretti ja tegi seda, mida tal kästi. Tema ema pani hoolega tähele kõike, mis oli juhtunud.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 Jeesus kasvas ja sai järjest targemaks ja tugevamaks ning oli Jumala ja inimeste soosingus.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.