< Roomlastele 11 >

1 Niisiis, ma küsin – kas Jumal on oma rahva kõrvale heitnud? Olen ju minagi iisraellane, Aabrahami järglane, Benjamini suguharust!
To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
2 Jumal ei ole oma rahvast, keda ta ette teadis, ära tõuganud. Pühakiri ütleb selles kohas Eelija kohta, kus ta anub Jumalat Iisraeli pärast:
Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
3 „Issand, nad on tapnud su prohvetid, lõhkunud maha su altarid! Mina üksi olen järgi jäänud ja nad püüavad mind tappa!“
“Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
4 Kuid mida Jumal talle vastas? „Ma olen jätnud endale seitse tuhat meest, kes ei ole kummardanud Baali ees.“
Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
5 Samuti on siis ka praegusel ajal olemas jääk, keda Jumal on armu tõttu valinud.
Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
6 Kui aga armust, siis mitte tegudest, sest muidu ei oleks arm enam arm.
In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
7 Mis me järeldame? Mida Iisrael taotleb, seda ta ei ole saanud kätte, aga äravalitud on selle kätte saanud. Ülejäänud on kalestunud,
To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
8 nagu on kirjutatud: „Jumal on andnud neile tardumuse vaimu, silmad, mis ei näe, ja kõrvad, mis ei kuule, kuni tänase päevani.“
kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
9 Ja Taavet ütleb: „Nende pidulaud saagu neile silmuseks ja lõksuks, püüniseks ja kättemaksuks!
Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
10 Löö nende silmi pimedusega, et nad ei näeks! Kõverda nende selg jäädavalt!“
Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
11 Seepärast ma küsin – kas Iisrael on komistanud, et kukkuda lõplikult? Kaugeltki mitte! Nende eksimuse tõttu on pääste saanud osaks mittejuutidele, et äratada Iisraelis kadedust.
Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
12 Aga kui nende eksimus tähendab rikkust kogu maailmale ja nende kaotamine rikkust mittejuutidele, siis kui palju suuremat rikkust toob nende täielik kaasamine?
Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
13 Ma räägin seda teie seas olevatele mittejuutidele. Kuna ma olen apostel mittejuutidele, olen ma uhke oma teenistuse üle,
Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
14 lootuses, et ma suudan ehk kuidagi äratada kadedust oma hõimlastes ning mõned neist päästa.
da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
15 Sest kui juba nende eemale tõukamine tõi maailmale lepituse, mida muud toob nende vastuvõtmine, kui elu tõusmist surmast?
Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
16 Aga kui uudsevili on püha, siis on seda kogu taigen. Ja kui juur on püha, siis on seda ka oksad.
In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
17 Aga kui mõned oksad on küljest murtud, sina aga kui metsõlipuu oled nende asemele poogitud ja saad osa õige õlipuu mahlakast juurest,
In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
18 siis ära hoople okste ees. Ja kui sa hoopled, siis pea meeles, et mitte sina ei kanna juurt, vaid juur kannab sind.
kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
19 Sina ehk ütled: „Oksad murti küljest, et mind asemele pookida.“
To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
20 Õige küll! Nemad murti küljest uskmatuse pärast, sina püsid puu küljes aga usu läbi. Ära mõtle kõrgilt, vaid karda!
Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
21 Kui Jumal ei jätnud karistamata loomupäraseid oksi, ei säästa ta sindki!
Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
22 Seepärast, pane tähele Jumala lahkust ja karmust: karmust nende suhtes, kes langevad, aga lahkust sinu vastu, kui sa püsid tema lahkuses; vastasel korral raiutakse sindki maha.
Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
23 Aga ka iisraellased, kui nad ei jää oma uskmatusse, poogitakse puu külge, sest Jumal suudab neid tagasi pookida.
In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
24 Sest kui juba sind metsõlipuu küljest lahti raiuti ja vastupidiselt loomulikule aedõlipuu külge poogiti, eks poogita loomupärased oksad seda enam nende oma puu külge.
Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
25 Vennad ja õed, et te ei oleks enda meelest targad, tahan ma teile teada anda saladuse: üht osa Iisraeli on tabanud kalestumine seni, kuni mittejuutide koguarv on sisse astunud.
Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
26 Ja nõnda päästetakse kogu Iisrael. Nagu on kirjutatud: „Siionist saabub Päästja, kes kõrvaldab Jaakobist jumalakartmatuse.
Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
27 See on minu leping nendega, kui ma kustutan ära nende patud.“
Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
28 Evangeeliumi seisukohalt on nad Jumala vaenlased teie heaks, aga Jumala valiku seisukohalt on nad armastatud esiisade pärast,
Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
29 sest Jumal ei võta tagasi oma armuande ja kutsumist!
gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
30 Sest nõnda nagu teie kord olite Jumalale sõnakuulmatud, aga nüüd olete armu saanud nende sõnakuulmatuse tõttu,
Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
31 nii on nüüd ka nemad muutunud sõnakuulmatuks teile osaks saanud halastuse pärast, et nendegi peale halastataks.
haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
32 Sest Jumal on kõik inimesed kinni pannud sõnakuulmatuse alla, et kõikide peale halastada. (eleēsē g1653)
Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē g1653)
33 Kui mõõtmatu on Jumala rikkuse, tarkuse ja teadmise sügavus! Kui läbiuurimatud on tema otsused ja kui mõistatuslikud on tema teed!
Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
34 „Sest kes on ära tundnud Issanda meele? Kes on olnud tema nõuandjaks?“
“Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
35 „Kes on midagi kunagi Jumalale andnud, et ta peaks talle tagasi maksma?“
“Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
36 Sest temast on tekkinud kõik, tema kaudu ja tema jaoks on olemas kõik. Temale kuulub kirkus igavesti! Aamen. (aiōn g165)
Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn g165)

< Roomlastele 11 >