< Ilmutus 16 >

1 Ma kuulsin templist võimsat häält ütlemas seitsmele inglile: „Minge ja valage maa peale välja seitse Jumala vihakaussi!“
Sai na ji wata babbar murya daga haikalin tana ce wa mala’iku bakwai nan, “Ku tafi ku zuba kwanoni bakwai nan na fushin Allah a kan duniya.”
2 Esimene ingel läks ja valas oma kausi välja maa peale, ning koledad ja mädased paised tekkisid inimeste kehale, kellel oli metsalise märk ja kes kummardasid tema kuju.
Mala’ika na fari ya je ya juye kwanonsa a bisan ƙasa, sai munanan gyambuna masu zafi suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar suka kuma yi wa siffarta sujada.
3 Teine ingel läks ja valas oma kausi välja merre, ning see muutus otsekui surnu vereks ja kõik elusolendid meres surid.
Mala’ika na biyu ya juye kwanonsa a bisan teku, sai tekun ya zama jini kamar na mataccen mutum, kuma kowane abu mai rai da yake cikin tekun ya mutu.
4 Kolmas valas oma kausi välja jõgedesse ja veeallikatesse ning need muutusid vereks.
Mala’ika na uku ya juye kwanonsa a bisan koguna da maɓulɓulan ruwa, sai suka zama jini.
5 Ja ma kuulsin inglit, kes vastutas vete eest, ütlevat: „Õige oled sina selles kohtumõistmises, sina Püha, kes oled ja kes olid;
Sa’an nan na ji mala’ikan da yake lura da ruwaye ya ce, “Kai mai adalci ne cikin waɗannan hukuntai, kai da kake yanzu, kake kuma a dā, Mai Tsarki, saboda yadda ka yi hukuncin nan;
6 sest nemad on valanud pühade ja prohvetite verd ning verd oled sina andnud neile juua, nagu nad seda väärivad.“
gama sun zub da jinin tsarkakanka da kuma annabawanka, ka kuwa ba su jini su sha, yadda ya dace da su.”
7 Ja ma kuulsin, kuidas altar ütles: „Jah, Issand Jumal, Kõigeväeline, tõelised ja õiged on sinu kohtuotsused!“
Na kuma ji bagaden ya amsa, “I, Ubangiji Allah, Maɗaukaki, hukuntanka daidai yake na adalci ne kuma.”
8 Neljas ingel valas oma kausi välja päikese peale, ning temale anti kõrvetada inimesi tulega.
Mala’ika na huɗu ya juye kwanonsa a bisan rana, sai aka ba wa rana iko ta ƙona mutane da wuta.
9 Suur kuumus kõrvetas inimesi ning nad teotasid Jumalat, kellel oli meelevald nende nuhtluste üle. Ja nad ei parandanud meelt, et anda austust Jumalale.
Aka ƙone su da zafin wuta mai tsanani suka kuwa la’anci sunan Allah wanda yake da iko a kan waɗannan annoban, amma suka ƙi su tuba su kuma ɗaukaka shi.
10 Viies ingel valas oma kausi välja metsalise trooni peale, ning tema kuningriik mattus pimedusse ja tema alamad närisid valu pärast keelt.
Mala’ika na biyar ya juye kwanonsa a bisan gadon sarautar dabbar, mulkinta kuwa ya zama duhu. Mutane suka yi ta cizon bakinsu saboda azaba
11 Nad teotasid taeva Jumalat oma valude ja paisete pärast, ega parandanud meelt oma tegudest.
suka kuma la’anci Allah na sama saboda zafinsu, da kuma saboda gyambunansu, amma suka ƙi su tuba daga abin da suka riga suka yi.
12 Kuues ingel valas oma kausi tühjaks suure Eufrati jõe peale, ning selle vesi kuivas ära, et anda teed idamaa kuningatele.
Mala’ika na shida ya juye kwanonsa a bisan babban kogin Yuferites, sai ruwansa ya shanye don a shirya hanya saboda sarakuna daga Gabas.
13 Ja ma nägin, kuidas lohe suust, metsalise suust ja valeprohveti suust väljus kolm rüvedat vaimu otsekui konnad.
Sa’an nan na ga mugayen ruhohi guda uku da suka yi kamar kwaɗi; suka fito daga bakin macijin nan, da kuma daga bakin dabbar, da kuma daga bakin annabin ƙaryan nan.
14 Need on tunnusmärke tegevad deemonlikud vaimud, kes lähevad laiali kogu maailma kuningate juurde, et koondada neid lahinguks, mis peab toimuma Kõigeväelise Jumala suurel päeval.
Su ruhohin aljanu ne da suke aikata abubuwan banmamaki, sukan je wurin sarakunan dukan duniya, don su tattara su don yaƙi a babbar ranar Allah Maɗaukaki.
15 „Vaata, ma tulen kui varas! Õnnis on inimene, kes valvab ning hoiab oma riideid, et ta ei käiks alasti, ja et ei nähtaks tema häbi.“
“Ga shi, ina zuwa kamar ɓarawo! Mai albarka ne wanda yake zama a faɗake yana kuma saye da tufafinsa, don kada yă yi tafiya tsirara a kuma kunyata shi.”
16 Ja nad koondati paika, mida heebrea keeles kutsutakse Harmagedoon.
Sa’an nan aka tattara sarakuna zuwa wurin da a Ibraniyanci ake kira Armageddon.
17 Seitsmes ingel valas oma kausi välja õhku, ning vali hääl kostis templis olevalt troonilt: „See on sündinud!“
Mala’ika na bakwai ya juye kwanonsa cikin iska, daga haikalin kuwa sai aka ji wata babbar murya daga kursiyin, tana cewa, “An gama!”
18 Siis sähvis välke, sündis hääli ja müristamisi ning suur maavärin, mille taolist ei ole olnud sellest ajast, kui inimesed on elanud maa peal – nii võimas oli see maavärin.
Sai ga walƙiya, ƙararraki, tsawa da kuma matsananciyar girgizar ƙasa. Ba a taɓa yin irin wannan girgizar ƙasar ba, tun kasancewar mutum a duniya, girgizar ƙasar kuwa gawurtacciya ce.
19 Ja suur linn jagunes kolmeks osaks ning rahvaste linnad varisesid rusuks. Suurt Paabelit tuletati meelde Jumala ees, et Jumal annaks temale juua oma raevuveini karikat.
Babban birnin ya rabu kashi uku, biranen al’ummai kuma suka rurrushe. Allah ya tuna da Babilon Mai Girma ya kuma ba ta kwaf cike da ruwan inabin fushinsa.
20 Kõik saared põgenesid ning mäed kadusid.
Kowane tsibiri ya gudu ba a kuwa ƙara ganin duwatsu ba.
21 Ja talendiraskusi raheteri sadas taevast maha inimeste peale, aga inimesed teotasid Jumalat rahenuhtluse pärast, sest see nuhtlus oli väga ränk.
Daga sararin sama manyan ƙanƙara masu nauyin gaske suka fāɗo a kan mutane. Suka kuma la’anci Allah saboda annobar ƙanƙarar, domin annobar ta yi muni ƙwarai.

< Ilmutus 16 >