< Markuse 2 >
1 Mõni päev hiljem tuli Jeesus taas Kapernauma. Kui saadi kuulda, et ta on kodus,
Bayan’yan kwanaki, da Yesu ya sāke shiga Kafarnahum, sai mutane suka ji labarin zuwansa gida.
2 kogunes palju rahvast, nii et isegi väljas ukse ees ei olnud enam ruumi. Ja Jeesus kõneles neile Jumala sõna.
Mutane suka taru da yawa har ma babu wuri, ko a bakin ƙofa ma, sai ya yi musu wa’azin bishara.
3 Siis tulid tema juurde neli meest, kes kandsid halvatut.
Waɗansu mutum huɗu suka zo wajensa ɗauke da wani shanyayye.
4 Ja kui nad rahvarohkuse tõttu ei pääsenud halvatuga talle ligi, tegid nad Jeesuse pea kohal katusesse avause ja lasksid alla magamisaseme, millel halvatu lamas.
Da ba su iya kai shi wurin Yesu ba, saboda taron, sai suka buɗe rufin gidan saman, bisa daidai inda Yesu yake. Bayan da suka huda rami, sai suka saukar da shanyayyen, kwance a kan tabarmarsa.
5 Nende usku nähes ütles Jeesus halvatule: „Poeg, sinu patud on sulle andeks antud!“
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Saurayi, an gafarta zunubanka.”
6 Aga seal istusid mõned kirjatundjad ja need mõtlesid iseeneses:
To, waɗansu malaman dokoki da suke zaune a wurin, suka yi tunani a zuciyarsu, suna cewa,
7 „Kuidas see mees võib öelda nõnda? Ta teotab Jumalat! Kes veel võib patte andeks anda kui vaid Jumal üksi?“
“Me ya sa mutumin nan yake magana haka? Yana saɓo! Wane ne zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
8 Kuid Jeesus teadis kohe oma vaimus, et nad niimoodi oma südames mõtlevad, ja ta ütles neile: „Miks te nõnda mõtlete?
Nan da nan, Yesu ya gane a ruhunsa abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya ce musu, “Me ya sa kuke tunanin waɗannan abubuwa?
9 Kumb on kergem, kas öelda halvatule „Sinu patud on andeks antud“või öelda talle „Tõuse üles, võta oma ase ja kõnni“?
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta zunubanka,’ ko a ce, ‘Tashi, ɗauki tabarmarka ka yi tafiya’?
10 Aga teadke, et Inimese Pojal on meelevald patte andeks anda maa peal!“Ja ta ütles halvatule:
Amma don ku san cewa, Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen,
11 „Tõuse üles, võta oma ase ja mine koju!“
“Ina ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka, ka tafi gida.”
12 Sedamaid tõusis mees üles, võttis oma magamisaseme ja väljus kõigi nähes, nii et kõik hämmastusid ja ülistasid Jumalat, öeldes: „Midagi sellist pole me kunagi näinud!“
Sai ya tashi, ya ɗauki tabarmarsa, ya yi tafiyarsa a gabansu duka. Wannan ya ba wa kowa mamaki, suka kuma ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin abu haka ba!”
13 Jeesus läks taas välja järve äärde ja ta juurde kogunes rahvahulk ja ta õpetas neid.
Yesu ya sāke tafiya bakin tafkin. Taro mai yawa ya zo wurinsa, sai ya fara koya musu.
14 Edasi minnes nägi ta Leevit, Alfeuse poega, maksukoguja pingil istumas ja ütles talle: „Järgne mulle!“Ja Leevi tõusis ja järgnes talle.
Yana cikin tafiya, sai ya ga Lawi, ɗan Alfayus zaune a inda ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” Sai Lawi ya tashi, ya bi shi.
15 Kui siis Jeesus istus lauas tema kodus, oli ka hulk maksukogujaid ja patuseid söömas koos tema ja ta jüngritega, sest paljud järgnesid talle.
Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Lawi, sai masu karɓar haraji da “masu zunubi” da yawa, suka zo suka ci tare da shi da almajiransa, gama akwai mutane da yawa da suka bi shi.
16 Ja kui variseride kirjatundjad nägid, et Jeesus sööb koos patuste ja maksukogujatega, ütlesid nad tema jüngritele: „Miks ta sööb koos maksukogujate ja patustega?“
Da malaman dokoki, waɗanda su ma Farisiyawa ne, suka ga yana ci tare da masu “zunubi” da masu karɓar haraji, sai suka tambayi almajiransa, suka ce, “Me ya sa yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
17 Seda kuuldes ütles Jeesus neile: „Arsti ei vaja terved, vaid haiged. Ma pole tulnud kutsuma õigeid, vaid patuseid.“
Da jin wannan, Yesu ya ce musu, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. Ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
18 Johannese jüngrid ja variserid pidasid aga parajasti paastu. Siis tulid mõned inimesed Jeesuse juurde ja küsisid: „Miks Johannese jüngrid ja variseride jüngrid paastuvad, aga sinu jüngrid ei paastu?“
To, almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, sai waɗansu mutane suka zo suka tambayi Yesu, suka ce, “Yaya almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
19 Jeesus vastas neile: „Ei sobi pulmalistel leinata ajal, kui peigmees on nende juures! Niikaua kui peigmees on nende juures, nad ei või paastuda.
Yesu ya amsa ya ce, “Yaya abokan ango za su yi azumi, sa’ad da yana tare da su? Ai, ba za su yi ba, muddin yana tare da su.
20 Kuid tuleb aeg, mil peigmees neilt ära võetakse, küll nad siis sel päeval paastuvad.
Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.
21 Keegi ei õmble vanutamata riidetükki paigaks vanale rõivale, muidu rebeneb vana rõivas uue paiga servast ja auk läheb suuremaks.
“Ba mai facin sabon ƙyalle a tsohuwar riga. In ya yi haka, sabon ƙyallen zai yage daga tsohuwar, yagewar kuwa za tă zama da muni.
22 Ka ei vala keegi värsket veini vanadesse nahklähkritesse, muidu vein pressib lähkrid lõhki ning siis ollakse ilma nii veinist kui lähkritest. Värske vein valatakse uutesse nahklähkritesse.“
Ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ya yi haka, ruwan inabin zai farfashe salkunan, yă yi hasarar ruwan inabin, salkunan kuma su lalace. A’a, yakan zuba sabon ruwan inabin a sababbin salkuna.”
23 Ühel hingamispäeval juhtus Jeesus minema läbi viljapõldude ja ta jüngrid hakkasid teed käies viljapäid katkuma.
Wata ranar Asabbaci, Yesu yana ratsa gonakin hatsi, sai almajiransa da suke tafiya tare da shi, suka fara kakkarya waɗansu kan hatsi.
24 Ja variserid ütlesid Jeesusele: „Vaata neid! Miks nad teevad seda, mida hingamispäeval teha ei tohi?“
Farisiyawa suka ce masa, “Duba, me ya sa suke yin abin da doka ta hana a yi, a ranar Asabbaci?”
25 Jeesus vastas neile: „Kas te pole kunagi lugenud, mida tegi Taavet, kui tal oli puudus ning tema ja ta kaaslased olid näljas?
Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa, suna kuma cikin bukata?
26 Ta läks Jumala kotta ülempreester Ebjatari päevil ning sõi ära ohvrileivad, mida oli lubatud süüa ainult preestritel. Ja ta andis ka oma kaaslastele.“
Ya shiga gidan Allah a zamanin Abiyatar babban firist, ya ci keɓaɓɓen burodin nan, ya kuma ba wa abokan tafiyarsa abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka?”
27 Ja Jeesus ütles neile: „Hingamispäev on seatud inimese jaoks, mitte inimene hingamispäeva jaoks.
Sai ya ce musu, “An yi Asabbaci saboda mutum ne, ba mutum saboda Asabbaci ba.
28 Seepärast on Inimese Poeg ka hingamispäeva Issand!“
Don haka, Ɗan Mutum Ubangiji ne, har ma da na Asabbaci.”