< Luuka 12 >
1 Vahepeal, kui kokku oli kogunenud mitmetuhandeline rahvahulk, nii et üksteise peal tallati, kõneles Jeesus esmalt oma jüngritele: „Olge valvel variseride juuretise pärast, mis on silmakirjalikkus!
Da jimawa kadan, bayan da mutane da yawa suka taru kwarai har suna tattaka junansu. Sai ya fara yin magana da almajiransa. “Ku yi lura da yisti na Farisawa, wanda shine manufunci.
2 Midagi ei ole varjatut, mida ei paljastataks, ega salajast, mis teatavaks ei saaks.
Amma ba abin da ke rufe wanda ba za a tone ba, ba kuma abin da ke boye wanda ba za a sani ba.
3 Mis te olete pimedas öelnud, saab kuuldavaks valges, ja mida te kõrva sosistate salakambrites, seda kuulutatakse katustelt.
Saboda haka ba abin da za ku fadi a asirce wanda ba za a ji shi a cikin sarari ba. Abin da ku ka fadi da rada cikin lungu, za a yi shelarsa a ko'ina.
4 Ma ütlen teile, sõbrad, ärge kartke neid, kes ihu tapavad ja pärast seda ei saa midagi teha!
Ina gaya maku abokaina, kada ku ji tsoron wanda da za su kashe jiki. Bayan haka kuma ba abin da za su iya yi.
5 Aga ma näitan teile, keda te peate kartma: kartke teda, kellel on meelevald teid pärast tapmist heita põrgusse! Jah, ma ütlen teile, teda kartke! (Geenna )
Bari in gargade ku a kan wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron shi wanda bayan ya kashe zai iya jefa ku cikin jahannama. I, ina ce maku ku ji tsoronsa. (Geenna )
6 Kas ei müüda viit varblast kahe penni eest? Ometi pole Jumal unustanud ühtki neist.
Ba a kan sayar da 'yan tsuntsaye biyar a kan anini biyu ba? Duk da haka, Allah ba zai manta da ko daya daga cikinsu ba.
7 Ent teie juuksekarvadki on kõik ära loetud. Ärge kartke, te olete rohkem väärt kui palju varblasi.
Har ma gashin da ke kan ku ya san yawan su. Kada ku ji tsoro, ku kun fi tsuntsaye daraja a wurinsa.
8 Ma ütlen teile, et igaüks, kes mind tunnistab inimeste ees, teda tunnistab ka Inimese Poeg Jumala inglite ees.
Ina gaya maku, dukan wanda za ya shaida ni a gaban mutane, Dan Mutum kuma za ya shaida shi a gaban mala'kun Allah.
9 Aga kes mind ära salgab inimeste ees, salatakse ära ka Jumala inglite ees.
Kuma dukan wanda ya ki ni a gaban mutane, za a ki shi a gaban mala'ikun Allah.
10 Igaühele, kes ütleb sõna Inimese Poja vastu, antakse andeks, aga kes teotab Püha Vaimu, sellele ei andestata.
Dukan wanda ya yi magana gaba da Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma shi wanda ya yi sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
11 Kui teid viiakse sünagoogidesse ning võimude ja valitsejate ette, siis ärge muretsege, kuidas end kaitsta või mida öelda,
Idan suka kawo ku gaban majami'a, ko gaban masu shari'a, ko gaban masu iko, kada ku damu da abin da za ku fada domin ku kare kanku. Ko kuwa abin da za ku ce.
12 sest sel hetkel õpetab Püha Vaim teile, mida te peate ütlema.“
Gama Ruhu Mai Tsarki zai koya maku abin da za ku fadi a wannan lokaci.”
13 Keegi rahva seast ütles talle: „Õpetaja, käsi mu vennal jagada pärandus minuga!“
Sai wani a cikin taron ya ce masa, “Malam, ka yi wa dan'uwana magana ya raba gado da ni
14 Jeesus vastas: „Kes mind on määranud teie vahele kohtunikuks või õigusemõistjaks?“
Yesu ya ce masa, “Kai, wanene ya sa ni in zama alkali, ko matsakanci a kanku?”
15 Siis ta ütles neile: „Olge valvel igasuguse ahnuse pärast, sest inimese elu ei seisne tema omandi külluses.“
Sai kuma ya ce masu, “Ku yi lura kada ku zama masu hadama, gama ba abin da mutum ya mallaka ne ya fi mahimmanci a cikin rayuwar sa ba.”
16 Ja siis ta rääkis neile tähendamissõna: „Ühe rikka mehe põld andis hea saagi.
Sa'annan Yesu ya fada masu wani misali, ya ce, “Gonar wani mutum ta bada amfani sosai,
17 Ta mõtles endamisi: „Mida ma pean tegema? Mul pole kuhugi oma saaki panna.“
ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?'
18 Ja ta ütles: „Ma teen nii: ma lõhun maha oma aidad ja ehitan suuremad, kuhu ma kogun vilja ülejäägi.
Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa.
19 Ja ma ütlen iseendale: „Sul on kõrvale pandud külluses vara paljudeks aastateks. Puhka, söö, joo ja ole rõõmus!““
Sai in ce da raina, “Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna.”
20 Aga Jumal ütles talle: „Sina rumal! Selsamal ööl võetakse sinult su elu. Aga kes saab siis selle, mis sa oled endale soetanud?“
Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?'
21 Nii on igaühega, kes kogub asju enda jaoks, kuid ei ole rikas Jumalas.“
Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah.”
22 Siis Jeesus ütles jüngritele: „Seepärast ma ütlen teile, ärge muretsege oma elu pärast, mida süüa, ega ihu pärast, mida selga panna,
Yesu, ya ce da almajiransa, “Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku.
23 sest elu on enam kui toit ja ihu enam kui rõivad.
Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
24 Vaadake kaarnaid – nad ei külva ega lõika, neil ei ole hoiuruumi ega aita, ometi Jumal toidab neid. Kui palju enam väärt lindudest olete teie!
Ku dubi hankaki wadanda ba sa yin shuka, ba sa yin girbi. Ba su da rumbuna ko dakunan ajjiya, amma Allah ya na ciyar da su. Ku fa kun fi tsuntsaye daraja!
25 Aga kes teie seast suudaks muretsemisega ennast ühe küünragi pikemaks teha?
Wanene a cikinku ta wurin sha'awarsa za ya iya karawa kansa kwanaki?
26 Ja kui te seda väikest asja ei suuda, milleks siis teiste asjade pärast muretseda!
Idan ba ku iya yi wa kanku dan karamin abu ba, me ya sa za ku damu da sauran abubuwa?
27 Vaadake, kuidas lilled kasvavad! Nad ei tööta ega ketra. Siiski ma ütlen teile, isegi Saalomon kogu oma hiilguses ei olnud riietatud nii nagu igaüks neist.
Ku dubi furanni a daji - yadda suke yin girma. Ba su kan yi aiki ba, ba su kan yi kadi ba. Ina gaya maku, ko Sulaimanu, a cikin darajarsa, bai sa tufafin da suka fi nasu kyau ba.
28 Kui aga Jumal niimoodi riietab väljal rohtu, mis täna on, aga homme heidetakse tulle, kui palju enam ta riietab siis teid, te nõdrausulised!
Idan Allah ya sa wa ciyawa tufafi masu kyau haka, wadda yau tana nan, gobe kuma a sa ta a wuta, ta yaya zai kasa sa maku tufafi, ku masu kankantar bangaskiya!
29 Ärge muretsege selle pärast, mida süüa või juua, ärge vaevake ennast sellega.
Kada ku damu da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kuma kada ku yi alhini.
30 Sest kõigi nende asjade järel jookseb paganlik maailm, kuid teie Isa ju teab, et te seda vajate.
Gama dukan al'umman duniya suna neman wadannan abubuwa, kuma Ubanku ya san kuna bukatar wada nan abubuwan.
31 Pigem otsige tema kuningriiki, ja see kõik antakse teile samuti!
Amma ku bidi mulkinsa, wadannan abubuwa kuma za a kara maku su.
32 Ära karda, väike karjake, sest teie Isal on hea meel anda teile kuningriik!
Kada ku ji tsoro, ku 'yan kanana, domin da murna Ubanku zai ba ku mulkin.
33 Müüge enda omand ja andke tulu vaestele! Varuge enesele kulumatud kukrud ja soetage püsiv varandus taevas, kuhu varas ei tule ja mida koi ei riku.
Ku sayar da abin da ku ke da shi ku ba matalauta. Kuyi wa kanku jakukkuna wadanda ba za su lalace ba, ku yi ajjiya cikin sama inda abin ba ya karewa, inda barayi ba za su iya zuwa ba, kwari kuma ba za su iya lalatawa ba.
34 Sest kus on su varandus, seal on ka su süda!
Domin inda dukiyarka take, can zuciyarka za ta kasance kuma.
35 Olge riietatud teenimiseks ja hoidke oma lambid põlemas
Ku rage tsawon tufafinku, ku yi dammara, ya zama fitilarku tana ci koyaushe,
36 nagu inimesed, kes ootavad isandat pulmapeolt koju. Et kui ta tuleb ja koputab, on nad otsekohe valmis talle ust avama.
ku kuma zama kamar wadanda suke jiran mai gidansu ya dawo daga gidan buki, domin duk sa'adda ya zo ya kwankwasa kofa, nan da nan za su bude masa.
37 Õnnistatud on need sulased, kelle isand saabudes leiab nad ootamas. Ma kinnitan teile: ta riietab end teenimiseks, paneb nad lauda istuma ja toidab neid.
Masu albarka ne wadannan bayi, wadanda ubangijinsu za ya tarar suna jiran dawowar sa. Gaskiya ni ke gaya ma ku, zai yi dammara yasa su zazzauna ya ba su abinci shi da kansa.
38 Õnnistatud on need sulased, kelle isand leiab nad valvamas, isegi kui ta tuleb teise või kolmanda vahikorra ajal öösel.
Ko da ubangijinsu ya zo da dare, ko da tsakar dare, ya tarar da su a shirye suna jiransa. Masu albarka ne wadannan bayi.
39 Küllap te mõistate, et kui peremees teaks, millisel öötunnil varas tuleb, ei laseks ta oma majja sisse murda.
Kuma ku san wannan, da mai gida ya san lokacin da barawo zai zo, ba zai bari a fasa masa gida a shiga ba.
40 Ka teie olge valmis, sest Inimese Poeg tuleb tunnil, mil te ei arvagi!“
Sai ku zauna da shiri fa domin ba ku san lokacin da Dan Mutum zai dawo ba.”
41 Peetrus küsis: „Issand, kas sa räägid seda tähendamissõna meile või kõikidele?“
Sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, mu ka ke fadawa wannan misali, ko ga kowa da kowa ne?”
42 Issand vastas: „Kes küll on ustav ja arukas majapidaja, kelle isand seab oma sulaste üle neid õigel ajal toitma?
Sai Ubangiji ya ce, “Wanne shugaba ne, mai aminci, mai hikima kuma wanda ubangijinsa za ya damka bayinsa a hannunsa, domin ya kula da su, ya ba su abincinsu a kan lokaci?
43 Õnnistatud on sulane, kelle ta isand tulles leiab nõnda tegevat!
Mai albarka ne wannan bawa, wanda ubangijinsa za ya tarar da shi yana yin abin da aka sa shi ya yi.
44 Tõesti, ma ütlen teile, ta annab tema hoolde kogu oma vara.
Hakika, ina gaya maku, zai danka dukan malakarsa a gareshi.
45 Aga kui see sulane mõtleb: „Mu isanda tulek viibib, “ning hakkab peksma teisi sulaseid ja tüdrukuid, sööma ja jooma ja purjutama,
Amma idan wannan bawa, ya ce a cikin zuciyarsa, 'Ubangiji na yayi jinkirin dawowa,' sai ya fara dukan bayin, maza da mata abokan bautarsa, ya ci ya sha, ya bugu,
46 siis selle sulase isand tuleb päeval, mil ta ei oota, ja tunnil, mida ta ei tea. Ta raiub sulase tükkideks ja annab talle sama koha uskmatutega.
ubangijin bawan nan zai dawo a lokacin da bawan bai sa tsammani ba, kuma a cikin lokacin da bai sani ba, ya daddatsa shi gunduwa-gunduwa, ya kuma hada shi da marasa aminci.
47 See sulane, kes küll teab oma isanda tahtmist, kuid ei valmistu ega tee tema tahtmise järgi, saab palju peksa.
Bawan nan, ya san halin ubagijinsa, amma bai shirya yayi abin da ubangijinsa yake so ba. Zai sha duka da bulala da yawa.
48 Kuid kes ei tea, aga teeb karistamist väärivaid asju, saab peksa vähem. Igaühelt, kellele on antud palju, nõutakse palju, ja kellele on usaldatud palju, sellelt küsitakse palju rohkem.
Amma shi wanda bai sani ba, kuma yayi abin da ba daidai ba, ba zai sha duka da bulala da yawa ba. Dukan wanda aka ba abu da yawa, za a kuma nemi abu da yawa daga wurinsa. Kuma ga wanda aka ba abu da yawa amana, za a nemi abu mafi yawa daga gareshi.
49 Tuld olen ma tulnud tooma maa peale, ja kuidas ma soovin, et see oleks juba süttinud!
Na zo domin in sa wuta a duniya, na so da ta riga ta kama.
50 Aga mul on vaja läbi minna ristimisest! Ja millise koorma all ma olen, kuni see on lõpetatud!
Amma ni, ina da baftisma wadda za a yi mani baftisma da ita, kuma na kagara, da an riga an yi ta!
51 Kas te arvate, et ma tulin rahu tooma maa peale? Ei, üldse mitte, vaid lahkmeelt.
Kuna zaton na zo duniya domin in kawo salama? Na ce maku a'a, amma tsattsaguwa.
52 Nüüdsest on ühes peres viis üksteise vastu lahkmeeles: kolm kahe vastu ja kaks kolme vastu.
Daga yanzu za a sami mutane biyar a cikin gida daya, kuma za su rarrabu, mutane uku suna gaba da biyu, biyun kuma suna gaba da ukun.
53 Lahkmeeles on isa poja vastu ja poeg isa vastu, ema tütre vastu ja tütar ema vastu, ämm minia vastu ja minia ämma vastu.“
Da da mahaifi za su yi gaba da juna, dan zai yi gaba da mahaifinsa. Mahaifiya za ta yi gaba da diyarta, diya kuma gaba da mahafiyarta; uwar miji za ta yi gaba da matar danta, matar da kuma gaba da uwar mijinta.”
54 Jeesus ütles ka rahvahulgale: „Kui te näete pilve tõusmas läänest, ütlete kohe: „Läheb vihmale.“Ja nii ta läheb.
Yesu, ya kuma gaya wa taron, “Da kun ga hadari ya taso daga yamma, nan da nan sai ku ce za a yi ruwa, haka kuwa ya kan zama.
55 Ja kui puhub lõunatuul, siis te ütlete: „Läheb palavaks.“Ja nõnda see on.
Idan iska tana busowa daga kudu sai ku ce za a yi zafi mai tsanani, haka kuwa ya kan faru.
56 Te silmakirjatsejad! Maa ja taeva ilmeid te teate, kuidas tõlgendada! Aga kuidas te siis praegust aega ei oska tõlgendada?
Munafukai, kun iya fasarta yanayin kasa da sama, amma baku iya fasarta abin da yake faruwa yanzu ba?
57 Miks te ise ei otsusta, mis on õige?
Me ya sa ba ku iya gane abin da zai tamake ku?
58 Kui sa oma vastasega lähed valitseja ette, püüa temaga ruttu teel olles ära leppida, et ta sind ei veaks kohtuniku juurde ja kohtunik ei annaks sind kohtuteenri kätte ja kohtuteener ei heidaks sind vanglasse.
Idan kuna tafiya wurin shari'a da abokin husumarka, ka yi kokari ku daidaita tun a kan hanya domin kada ya kai ka wurin mai shari'a. Domin kada mai shari'a ya mika ka ga mai tsaron kurkuku, shi kuwa mai tsaron kurkuku ba zai nuna maka sani a cikin kurkuku ba.
59 Ma ütlen sulle, sa ei pääse sealt enne, kui sa oled tagasi maksnud viimsegi veeringu.“
Na gaya maka, ba za ka iya fitowa ba sai ka biya dukan kudin da a ke binka?