< Jaakobuse 2 >
1 Vennad ja õed, ärge siduge oma usku meie kirkuse Issandasse Jeesusesse Kristusesse vahetegemisega inimeste vahel.
’Yan’uwana, a matsayinmu cikin Ubangiji Yesu Kiristi maɗaukaki, kada ku nuna bambanci.
2 Oletagem, et teie koosolekule tuleb kuldsõrmustega mees uhkeis rõivais ja tuleb ka räpases rõivais vaene.
A ce wani ya shigo cikin taronku saye da zoben zinariya da riguna masu tsada, wani matalauci kuma saye da tsummoki shi ma ya shigo,
3 Teie osutate austust sellele, kes kannab uhkeid rõivaid, ning ütlete talle: „Istuge siia, palun, “aga vaesele te ütlete: „Sina seisa seal!“või „Istu maha mu jalgade juurde!“
in kuka mai da hankali na musamman ga mutumin da yake da riguna masu tsadan nan kuka kuma ce, “Ga wurin zama mai kyau dominka,” amma kuka ce wa matalaucin nan, “Kai tsaya daga can,” ko kuwa, “Ka zauna a ƙasa kusa da ƙafafuna,”
4 Eks ole te siis teinud vahet omade seas ja saanud eelarvamustega otsustajateks?
ashe, ba ku nuna bambanci a tsakaninku ke nan ba, kuka kuma zama alƙalai masu mugayen tunani?
5 Kuulge, mu armsad vennad ja õed! Kas pole Jumal valinud maailma silmis vaeseid saama rikkaks usu poolest ja pärima Kuningriiki, mille tema on tõotanud neile, kes teda armastavad?
Ku saurara,’yan’uwana ƙaunatattu. Ashe, Allah bai zaɓi waɗanda suke matalauta a idon duniya don su zama masu wadata cikin bangaskiya, su kuma gāji mulkin da ya yi wa masu ƙaunarsa alkawari ba?
6 Teie aga olete halvustanud vaest! Kas mitte rikkad ei rõhu teid ega tõmba teid kohtusse?
Ga shi kun wulaƙanta matalauta. Ashe, ba masu arziki ne suke cutarku ba? Ba su ba ne suke jan ku zuwa kotu?
7 Kas ei teota just nemad seda kallist nime, millega teid on kutsutud?
Ba su ba ne suke ɓata sunan nan mai martaba wanda aka san ku da shi ba?
8 Kui te täidate kuninglikku seadust Pühakirja järgi „Armasta oma ligimest nagu iseennast!“, siis teete hästi.
In fa kun kiyaye dokan nan ta mulki wadda take cikin Nassi mai cewa, “Ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka,” kun yi daidai.
9 Aga kui te inimesi eelistate välise järgi, siis te teete pattu ja Seadus tunnistab teid üleastujaiks.
Amma in kuka nuna bambanci, kun yi zunubi ke nan shari’a kuma ta same ku da laifi a matsayin masu karya doka.
10 Sest igaüks, kes täidab kogu Seadust, kuid eksib ühe käsu vastu, on süüdi kõigis üleastumises.
Gama duk wanda ya kiyaye dukan doka amma ya yi tuntuɓe a kan abu ɗaya kaɗai, ya zama mai laifin karya dukansu ke nan.
11 On ju see, kes ütles: „Ära riku abielu!“, samuti öelnud: „Ära tapa!“Kui sa ei riku abielu, aga tapad, oled ikka seaduserikkuja.
Gama shi da ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisankai.” In kuwa ba ka zina amma kana kisankai, ka zama mai karya doka ke nan.
12 Nõnda siis rääkige ja käituge nagu need, kelle üle kord kohut mõistetakse vabaduse seaduse järgi.
Ku yi magana ku kuma yi aiki kamar waɗanda za a yi musu shari’a bisa ga doka mai ba da’yanci,
13 Sest kohus on halastamatu sellele, kes ise ei osuta halastust. Halastus aga on suurem kui kohus.
gama za a yi wa duk wanda bai nuna jinƙai ba hukunci babu jinƙai. Jinƙai yakan yi nasara a kan hukunci!
14 Mis kasu on sellest, mu vennad ja õed, kui keegi väidab endal olevat usku, aga tegusid ei ole? Ega seesugune usk või teda päästa?
Wanda amfani ne,’yan’uwana, a ce wani yă ce yana da bangaskiya, amma ba shi da ayyuka? Anya, wannan bangaskiya za tă iya cetonsa kuwa?
15 Kui teie vend või õde on ilma riieteta ja igapäevase toiduta,
A ce wani ɗan’uwa ko’yar’uwa ba shi da riguna ko abincin yini,
16 ja keegi teist ütleb talle: „Mine rahuga, pane soojalt riidesse ja söö kõht täis, “aga ei anna talle eluks vajalikku, mis on siis sellest kasu?
sai waninku yă ce masa, “Sauka lafiya, Allah ya ba da ci da sha da kuma sutura,” amma bai yi wani abu game da bukatunsa na jiki ba, ina amfani?
17 Nii on ka usuga: kui sel pole tegusid, on see iseenesest surnud.
Haka ma bangaskiya ita kaɗai, in ba tare da ayyuka ba, matacciya ce.
18 Kuid keegi võib öelda: „Sinul on usk ja minul on teod.“Näita mulle oma usku lahus tegudest ja mina näitan sulle oma usku koos tegudega.
Amma wani zai ce, “Kai kana da bangaskiya; ni kuma ina da ayyuka.” Ka nuna mini bangaskiyarka ba tare da ayyuka ba, ni kuma zan nuna maka bangaskiyata ta wurin abin da nake yi.
19 Sina usud, et Jumal on üksainus? Hästi teed! Ka deemonid usuvad seda ja värisevad hirmust.
Ka gaskata cewa Allah ɗaya ne. To, da kyau! Ai, ko aljanu ma sun gaskata wannan, har da rawan jiki.
20 Kas sa tahad tõendeid, oh taipamatu inimlaps, et usk ilma tegudeta on surnud?
Kai wawa, kana son tabbaci cewa bangaskiya marar ayyuka banza ce?
21 Eks mõistetud meie esiisa Aabraham Jumala ees õigeks tegude järgi, kui ta oma poja Iisaki viis ohvrialtarile?
Ashe, ba a mai da kakanmu Ibrahim mai adalci saboda abin da ya yi ba ne sa’ad da ya miƙa ɗansa Ishaku a bisa bagade?
22 Sa näed, et usk avaldus tema tegudes ja sai täiuslikuks tegude kaudu.
Ai, ka gani cewa bangaskiyarsa da ayyukansa sun yi aiki tare, bangaskiyarsa kuma ta zama cikakkiya ta wurin abin da ya yi.
23 Nii läks täide Pühakirja sõna: „Aabraham uskus Jumalat ja see arvati talle õiguseks, “ning teda hüüti Jumala sõbraks.
Aka kuma cika nassin nan da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne gare shi,” aka kuma ce da shi abokin Allah.
24 Näete siis, et inimene mõistetakse õigeks tegude järgi, mitte ainult usust.
Kun ga cewa ashe mutum zai sami kuɓuta ta wurin abin da ya yi ne ba ta wurin bangaskiya kaɗai ba.
25 Nõndasamuti mõisteti ka hoor Raahab õigeks tegude järgi, kui ta maakuulajad lahkelt vastu võttis ja nad teist teed linnast välja aitas.
Ta haka kuma ashe, Rahab karuwan nan ba a ɗauke ta mai adalci ce saboda abin da ta yi ba ne sa’ad da ta ba wa’yan leƙen asirin nan masauƙi ta kuma sallame su suka tafi ta wata hanya dabam?
26 Sest nii nagu ihu ilma vaimuta on surnud, on surnud ka usk ilma tegudeta.
Kamar yadda jikin da babu ruhu matacce ne, haka ma bangaskiyar da babu ayyuka matacciya ce.