< Heebrealastele 2 >

1 Seetõttu tuleb meil eriti silmas pidada kõike, mida me oleme kuulnud, et me ei kalduks kõrvale.
Dole mu ƙara mai da hankali sosai ga abubuwan da muka ji, don kada mu kauce.
2 Sest kui juba inglite kaudu räägitud sõnum oli kohustuslik ning iga üleastumine ja sõnakuulmatus sai karistuse,
Gama in saƙon da aka faɗi ta bakin mala’iku ya zama tabbatacce, kuma kowane ƙeta umarni da rashin biyayya suka karɓi sakamakonsu da ya dace,
3 kuidas siis meil õnnestuks põgeneda, kui me ei hooli nii suurest päästest, mida esmalt kuulutati Issanda enda suu läbi ja mida on kinnitanud need, kes seda kuulsid.
yaya za mu tsira in muka ƙyale irin wannan babban ceto? Wannan ceto, wanda Ubangiji ne ya fara sanar, aka kuma tabbatar mana ta bakin waɗanda suka ji shi.
4 Jumal on ju seda kinnitanud tunnustähtede, imede ja mitmesuguste võimsate tegudega ning Püha Vaimu andidega, mida ta jagas oma tahte kohaselt.
Allah shi ma ya shaida ta wurin alamu, abubuwan banmamaki da mu’ujizai iri-iri, da kuma baye-bayen Ruhu Mai Tsarki da aka rarraba bisa ga nufinsa.
5 Jumal ei alistanud inglitele tulevast maailma, millest me räägime.
Ba ga mala’iku ba ne ya sa su yi mulkin duniya mai zuwa, wanda muke magana a kai ba.
6 Pühakiri tunnistab sellest: „Mis on inimene, et sa temale mõtled, või inimese poeg, et sa temast hoolid?
Amma akwai wani wurin da wani ya shaida cewa, “Mene ne mutum, da kake tuna da shi, ɗan mutum da kake kula da shi?
7 Sa tegid ta veidi alamaks inglitest, sa pärgasid ta au ja hiilgusega,
Ka sa shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku; ka naɗa shi da ɗaukaka da girma,
8 ja alistasid kõik tema jalge alla.“Temale kõike alistades ei jätnud Jumal midagi talle alistamata. Aga praegu me ei näe veel, et kõik on alistatud tema alla.
ka kuma sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” Ta wurin sa kome a ƙarƙashinsa, Allah bai bar wani abu da bai sa a ƙarƙashinsa ba. Duk da haka a yanzu ba mu ga kowane abu a ƙarƙashinsa ba.
9 Siiski me näeme, et Jeesus, kes viivuks tehti alamaks inglitest, et ta Jumala armu läbi maitseks surma igaühe eest, on nüüd pärjatud au ja hiilgusega surma kannatamise pärast.
Sai dai muna ganin Yesu, wanda aka mai da shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku, yanzu kuwa an naɗa shi da ɗaukaka da girma domin yă sha wahalar mutuwa, domin ta wurin alherin Allah yă ɗanɗana mutuwa saboda kowa.
10 Sest Jumalale, kelle jaoks ja kelle läbi on kõik, oli kohane teha kannatuste kaudu täiuslikuks nende pääste teerajaja, selle, kes pidi viima kirkusesse palju lapsi.
Ta wurin kawo’ya’ya masu yawa zuwa ga ɗaukaka, ya dace cewa Allah, wanda dominsa da kuma ta wurinsa ne kome yake kasancewa, ya sa tushen cetonsu yă zama cikakke ta wurin shan wahala.
11 On ju nii pühitsejal kui ka pühitsetavail üks ja seesama Isa. Seepärast Jeesus ei häbenegi nimetada neid vendadeks ja õdedeks:
Da shi wanda yake tsarkake mutane da kuma su waɗanda ake tsarkakewa duk’yan iyali ɗaya ne. Saboda haka Yesu ba ya kunyan kiransu’yan’uwansa.
12 „Ma tahan kuulutada sinu nime oma vendadele, koguduse keskel tahan ma laulda sulle kiitust!“
Ya ce, “Zan sanar da sunanka ga’yan’uwana; a gaban jama’a zan rera yabonka.”
13 Ja veel: „Ma panen oma lootuse tema peale.“Ja veel: „Siin olen mina ja lapsed, kelle Jumal mulle on kinkinud.“
Har wa yau ya ce, “Zan dogara gare shi.” Ya kuma ce, “Ga ni, da’ya’yan da Allah ya ba ni.”
14 Sellepärast, kuna lapsed on lihast ja verest, sai temagi lihaks ja vereks, et surma läbi murda selle vägi, kes hoiab surma võimu – see tähendab kuradi –
Da yake’ya’yan suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamanninsu na mutum domin ta wurin mutuwarsa yă hallaka wanda yake riƙe da ikon mutuwa, wato, Iblis
15 ja vabastada kõik, kes olid kogu elu olnud surmahirmu orjuses.
ya kuma’yantar da waɗanda dukan rayuwarsu tsoron mutuwa ya riƙe su cikin bauta.
16 Sest kindlasti ei tulnud ta appi inglitele, vaid Aabrahami järglastele.
Gama tabbatacce ba mala’iku ne ya taimaka ba, sai dai zuriyar Ibrahim.
17 Seepärast ta pidi igas mõttes saama nende sarnaseks, et temast saaks halastav ja ustav ülempreester Jumala ees inimeste pattude lepitamiseks.
Saboda wannan dole a mai da shi kamar’yan’uwansa ta kowace hanya, domin yă zama babban firist mai aminci da mai jinƙai cikin hidima ga Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu saboda zunuban mutane.
18 Kuna ta ise on kannatanud ja tundnud kiusatusi, suudab ta aidata neid, kes on kiusatustes.
Domin shi kansa ya sha wahala sa’ad da aka gwada shi, yana iya taimakon waɗanda ake yi wa gwaji.

< Heebrealastele 2 >