< Koloslastele 1 >
1 Pauluselt, kes on Jumala tahtel Jeesuse Kristuse apostel, ja vend Timoteoselt,
Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,
2 Jumala pühadele Kolossas, ustavatele vendadele ja õdedele Kristuses: Armu ja rahu teile Jumalalt, meie Isalt!
Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi. Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.
3 Me täname Jumalat, meie Issanda Jeesuse Kristuse Isa, kui me teie eest palvetame,
Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku.
4 sest oleme kuulnud teie usust Kristusesse Jeesusesse ja armastusest kõigi pühade vastu
Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka.
5 lootuse pärast, mis on teie jaoks taevasse hoiule pandud. Sellest lootusest te olete juba kuulnud, kui evangeeliumi tõesõnum
Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar
6 teie juurde jõudis. Seesama evangeelium kannab nüüd vilja ja kasvab kogu maailmas, täpselt samamoodi, nagu on juhtunud teiegi juures alates päevast, mil te seda kuulsite ja hakkasite mõistma Jumala armu.
da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta.
7 Epafras, kes seda teile õpetas, on meie armas kaassulane ja Kristuse ustav teenija meie heaks.
Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu,
8 Tema rääkiski meile armastusest, mida Vaim on teis äratanud.
wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.
9 Seepärast ei ole me lakanud palvetamast ja anumast teie pärast alates päevast, mil me seda kuulsime, et teid täidetaks Jumala tahtmise tundmisega koos kõige vaimuliku tarkuse ja arusaamisega.
Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka.
10 Et te saaksite elada Issanda väärilist elu ja talle igati meeldida: kandes vilja kõiges heas töös, kasvades Jumala tundmises,
Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah.
11 saades vägevaks tema aulise väe läbi, et te oleksite vastupidavad ja kannatlikud,
Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki
12 tänades rõõmsalt Isa, kes on teid kõlbulikuks teinud osa saama pühade pärandist valguse kuningriigis.
kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske.
13 Sest tema on meid päästnud pimeduse meelevallast ning toonud meid oma armsa Poja Kuningriiki.
Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna,
14 Temas on meil lunastus, pattude andestus.
wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.
15 Tema on nähtamatu Jumala kuju, sündinud enne kõike loodut,
Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta.
16 sest tema läbi on loodud kõik, mis on taevastes ja maa peal, mis nähtav ja nähtamatu, olgu aujärjed, võimud, valitsused ja meelevallad – kõik on loodud tema läbi ja tema jaoks.
Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne.
17 Tema ise on enne kõike ja kõik püsib koos tema sees.
Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe.
18 Tema on oma ihu, koguduse pea. Ta on algus, esmasündinu surnute hulgast, et tema oleks ülim kõiges.
Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici.
19 Sest Jumal arvas heaks panna temasse kogu oma täiuse
Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi,
20 ja lepitada tema kaudu enesega kõik, kes on maa peal ja kes on taevas, sellega, et ta tegi rahu tema vere läbi, mis ristil valati.
ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.
21 Kunagi olite teiegi Jumalast võõrdunud ja mõtteviisi poolest tema vaenlased oma kurjade tegudega.
A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku.
22 Nüüd aga on Kristus teid lepitanud oma lihalikus ihus surma läbi, et saaksite seista pühadena, veatuina ja laitmatuina tema ees,
Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi.
23 kui te jätkate kindlana ja rajatuna usus ega tagane evangeeliumis olevast lootusest. See on evangeelium, mida te olete kuulnud ja mida on kuulutatud kogu loodule taeva all ja mille teenriks olen saanud ka mina, Paulus.
Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.
24 Nüüd on mul hea meel selle üle, mida ma teie pärast kannatan. Ja kui mu maises elus on veel midagi Kristuse vaevadest olemata, talun ma sedagi tema ihu, see on koguduse heaks.
Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya.
25 Jumal on määranud mind koguduse teenriks, et ma kuulutaksin teile Jumala sõna kogu selle täiuses,
Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai.
26 saladust, mis oli varjatud läbi aegade ja sugupõlvede, kuid mis nüüd on ilmutatud tema pühadele. (aiōn )
Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn )
27 Neile tahtis Jumal selle teatavaks teha ja näidata selle saladuse aulisi rikkusi kõigi rahvaste seas; see on Kristus teie sees, kirkuse lootus.
Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.
28 Teda me kuulutame, manitsedes ja õpetades igaüht kogu tarkuses, et valmistada ette iga inimest täiuslikuks Kristuses.
Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi.
29 Selle nimel ma võitlen ja pingutan Kristuse jõuga, mis minus väega tegutseb.
Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.