< Psalmaro 108 >
1 Kanto. Psalmo de David. Fortika estas mia koro, ho Dio; Mi kantos kaj gloros kun mia honoro.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Vekiĝu, psaltero kaj harpo; Mi vekos la matenan ĉielruĝon.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 Mi gloros Vin, ho Eternulo, inter la popoloj; Kaj mi prikantos Vin inter la gentoj.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 Ĉar granda ĝis super la ĉielo estas Via boneco, Kaj ĝis la nuboj estas Via vero.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Altiĝu super la ĉielo, ho Dio; Kaj Via gloro estu super la tuta tero.
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 Por ke liberiĝu viaj amatoj, Helpu per Via dekstra mano, kaj aŭskultu min.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 Dio diris en Sia sanktejo: Mi triumfos; Mi dividos Ŝeĥemon, kaj la valon Sukot Mi mezuros.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Al Mi apartenas Gilead, al Mi apartenas Manase; Efraim estas la forto de Mia kapo, Jehuda estas Mia sceptro.
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab estas Mia lavopelvo; Sur Edomon Mi ĵetos Mian ŝuon; Super Filiŝtujo Mi triumfe krios.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Kiu enkondukos min en fortikigitan urbon? Kiu alkondukos min ĝis Edom?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Ĉu ne Vi, ho Dio, forlasis nin? Vi ne eliras, ho Dio, kun niaj militistaroj.
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Donu al ni helpon kontraŭ la malamiko; Vanta estas helpo de homo.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 Kun Dio ni faros heroaĵojn; Kaj Li dispremos niajn malamikojn.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.