< Ruth 1 >

1 And it cometh to pass, in the days of the judging of the judges, that there is a famine in the land, and there goeth a man from Beth-Lehem-Judah to sojourn in the fields of Moab, he, and his wife, and his two sons.
A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
2 And the name of the man [is] Elimelech, and the name of his wife Naomi, and the name of his two sons Mahlon and Chilion, Ephrathites from Beth-Lehem-Judah; and they come into the fields of Moab, and are there.
Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
3 And Elimelech husband of Naomi dieth, and she is left, she and her two sons;
To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
4 and they take to them wives, Moabitesses: the name of the one [is] Orpah, and the name of the second Ruth; and they dwell there about ten years.
Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
5 And they die also, both of them — Mahlon and Chilion — and the woman is left of her two children and of her husband.
sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
6 And she riseth, she and her daughters-in-law, and turneth back from the fields of Moab, for she hath heard in the fields of Moab that God hath looked after His people, — to give to them bread.
Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
7 And she goeth out from the place where she hath been, and her two daughters-in-law with her, and they go in the way to turn back unto the land of Judah.
Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
8 And Naomi saith to her two daughters-in-law, 'Go, turn back, each to the house of her mother; Jehovah doth with you kindness as ye have done with the dead, and with me;
Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
9 Jehovah doth grant to you, and find ye rest each in the house of her husband;' and she kisseth them, and they lift up their voice and weep.
Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
10 And they say to her, 'Surely with thee we go back to thy people.'
suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
11 And Naomi saith, 'Turn back, my daughters; why do ye go with me? are there yet to me sons in my bowels that they have been to you for husbands?
Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
12 Turn back, my daughters, go, for I am too aged to be to a husband; though I had said, There is for me hope, also, I have been to-night to a husband, and also I have borne sons:
Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
13 for them do ye wait till that they grow up? for them do ye shut yourselves up, not to be to a husband? nay, my daughters, for more bitter to me than to you, for the hand of Jehovah hath gone out against me.'
za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
14 And they lift up their voice, and weep again, and Orpah kisseth her mother-in-law, and Ruth hath cleaved to her.
A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
15 And she saith, 'Lo, thy sister-in-law hath turned back unto her people, and unto her god, turn thou back after thy sister-in-law.'
Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
16 And Ruth saith, 'Urge me not to leave thee — to turn back from after thee; for whither thou goest I go, and where thou lodgest I lodge; thy people [is] my people, and thy God my God.
Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
17 Where thou diest I die, and there I am buried; thus doth Jehovah to me, and thus doth He add — for death itself doth part between me and thee.'
Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
18 And she seeth that she is strengthening herself to go with her, and she ceaseth to speak unto her;
Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
19 and they go both of them till their coming in to Beth-Lehem; and it cometh to pass at their coming in to Beth-Lehem, that all the city is moved at them, and they say, 'Is this Naomi?'
Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
20 And she saith unto them, 'Call me not Naomi; call me Mara, for the Almighty hath dealt very bitterly to me,
Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
21 I went out full, and empty hath Jehovah brought me back, why do ye call me Naomi, and Jehovah hath testified against me, and the Almighty hath done evil to me?'
In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
22 And Naomi turneth back, and Ruth the Moabitess her daughter-in-law with her, who hath turned back from the fields of Moab, and they have come in to Beth-Lehem at the commencement of barley-harvest.
Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.

< Ruth 1 >