< Ruth 2 >

1 And Naomi hath an acquaintance of her husband's, a man mighty in wealth, of the family of Elimelech, and his name [is] Boaz.
To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
2 And Ruth the Moabitess saith unto Naomi, 'Let me go, I pray thee, into the field, and I gather among the ears of corn after him in whose eyes I find grace;' and she saith to her, 'Go, my daughter.'
Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
3 And she goeth and cometh and gathereth in a field after the reapers, and her chance happeneth — the portion of the field is Boaz's who [is] of the family of Elimelech.
Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
4 And lo, Boaz hath come from Beth-Lehem, and saith to the reapers, 'Jehovah [is] with you;' and they say to him, 'Jehovah doth bless thee.'
Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
5 And Boaz saith to his young man who is set over the reapers, 'Whose [is] this young person?'
Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
6 And the young man who is set over the reapers answereth and saith, 'A young woman — Moabitess — she [is], who came back with Naomi from the fields of Moab,
Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
7 and she saith, Let me glean, I pray thee — and I have gathered among the sheaves after the reapers; and she cometh and remaineth since the morning and till now; she sat in the house a little.
Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
8 And Boaz saith unto Ruth, 'Hast thou not heard, my daughter? go not to glean in another field, and also, pass not over from this, and thus thou dost cleave to my young women:
Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
9 thine eyes [are] on the field which they reap, and thou hast gone after them; have not I charged the young men not to touch thee? when thou art athirst then thou hast gone unto the vessels, and hast drunk from that which the young men draw.'
Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
10 And she falleth on her face, and boweth herself to the earth, and saith unto him, 'Wherefore have I found grace in thine eyes, to discern me, and I a stranger?'
Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
11 And Boaz answereth and saith to her, 'It hath thoroughly been declared to me all that thou hast done with thy mother-in-law, after the death of thy husband, and thou dost leave thy father, and thy mother, and the land of thy birth, and dost come in unto a people which thou hast not known heretofore.
Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
12 Jehovah doth recompense thy work, and thy reward is complete from Jehovah, God of Israel, under whose wings thou hast come to take refuge.'
Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
13 And she saith, 'Let me find grace in thine eyes, my lord, because thou hast comforted me, and because thou hast spoken unto the heart of thy maid-servant, and I — I am not as one of thy maid-servants.'
Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
14 And Boaz saith to her, 'At meal-time come nigh hither, and thou hast eaten of the bread, and dipped thy morsel in the vinegar.' And she sitteth at the side of the reapers, and he reacheth to her roasted corn, and she eateth, and is satisfied, and leaveth.
A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
15 And she riseth to glean, and Boaz chargeth his young men, saying, 'Even between the sheaves she doth glean, and ye do not cause her to blush;
Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
16 and also ye do surely cast to her of the handfuls — and have left, and she hath gleaned, and ye do not push against her.'
Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
17 And she gleaneth in the field till the evening, and beateth out that which she hath gleaned, and it is about an ephah of barley;
Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
18 and she taketh [it] up, and goeth into the city, and her mother-in-law seeth that which she hath gleaned, and she bringeth out and giveth to her that which she left from her satiety.
Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
19 And her mother-in-law saith to her, 'Where hast thou gleaned to-day? and where hast thou wrought? may he who is discerning thee be blessed.' And she declareth to her mother-in-law with whom she hath wrought, and saith, 'The name of the man with whom I have wrought to-day [is] Boaz.'
Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
20 And Naomi saith to her daughter-in-law, 'Blessed [is] he of Jehovah who hath not forsaken His kindness with the living and with the dead;' and Naomi saith to her, 'The man is a relation of ours; he [is] of our redeemers.'
Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
21 And Ruth the Moabitess saith, 'Also he surely said unto me, Near the young people whom I have thou dost cleave till they have completed the whole of the harvest which I have.'
Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
22 And Naomi saith unto Ruth her daughter-in-law, 'Good, my daughter, that thou goest out with his young women, and they come not against thee in another field.'
Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
23 And she cleaveth to the young women of Boaz to glean, till the completion of the barley-harvest, and of the wheat-harvest, and she dwelleth with her mother-in-law.
Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.

< Ruth 2 >