< Romans 9 >

1 Truth I say in Christ, I lie not, my conscience bearing testimony with me in the Holy Spirit,
Gaskiya ne nake gaskiya nake fada cikin Almasihu. Ba karya nake yi ba. Lamirina, na shaida a cikin Ruhu Mai Tsarki.
2 that I have great grief and unceasing pain in my heart —
cewa ina da matukar bakin-ciki da takaici marar karewa a zuciyata.
3 for I was wishing, I myself, to be anathema from the Christ — for my brethren, my kindred, according to the flesh,
Dama ace, a la'anta ni, in rabu da Almasihu saboda 'yan'uwana, wato dangina da suke zuriyata bisa ga jiki.
4 who are Israelites, whose [is] the adoption, and the glory, and the covenants, and the lawgiving, and the service, and the promises,
Sune Isra'ilawa, sun sami karbuwa, da daukaka, da baiwar shari'a, da yi wa Allah sujada, da alkawarai.
5 whose [are] the fathers, and of whom [is] the Christ, according to the flesh, who is over all, God blessed to the ages. Amen. (aiōn g165)
Dukkan ubanni nasu ne daga cikinsu Almasihu ya fito bisa ga jiki- wanda shi ke Allah bisa kowa. Yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin. (aiōn g165)
6 And it is not possible that the word of God hath failed; for not all who [are] of Israel are these Israel;
Amma ba wai alkawarin Allah ya kasa ba ne, ba dukkan Isra'ilawa ne suke Isra'ilawa na gaskiya ba.
7 nor because they are seed of Abraham [are] all children, but — 'in Isaac shall a seed be called to thee;'
Haka nan, ba dukkan zuriyar Ibrahim ne 'ya'yansa ba. Amma ''ta wurin Ishiyaku ne za'a kira zuriyarka.''
8 that is, the children of the flesh — these [are] not children of God; but the children of the promise are reckoned for seed;
Yana nuna mana cewa ba 'ya'yan jiki su ne 'ya'yan Allah ba. Amma 'ya'yan alkawari ne ake kirga su, kuma aka kebe su.
9 for the word of promise [is] this; 'According to this time I will come, and there shall be to Sarah a son.'
Wanna ce kalmar alkawari, ''badi warhaka zan dawo, Saratu kuwa zata sami da.''
10 And not only [so], but also Rebecca, having conceived by one — Isaac our father —
Amma ba wannan kadai ba, bayan Rifkatu ta dauki ciki daga gun mijinta, ubammu Ishiyaku.
11 (for they being not yet born, neither having done anything good or evil, that the purpose of God, according to choice, might remain; not of works, but of Him who is calling, ) it was said to her —
Yaran nan kafin ma a haife su, balle ma a ce sun yi wani abu mai kyau ko laifi, saboda zaben da Allah yayi, bai danganta da abin da suka yi ba, ko don aiki ba, amma don shine mai kira—
12 'The greater shall serve the less;'
kamar yadda Ya ce, mata, “babban zaya yiwa karamin bauta,'' haka nassi yace,
13 according as it hath been written, 'Jacob I did love, and Esau I did hate.'
''Kamar yadda aka rubuta: “Yakubu na ke kauna, amma Isuwa na ki shi.”
14 What, then, shall we say? unrighteousness [is] with God? let it not be!
To me zamu ce kenan? Allah ya yi rashin adalci kenan? Ko kadan.
15 for to Moses He saith, 'I will do kindness to whom I do kindness, and I will have compassion on whom I have compassion;'
Gama ya ce wa Musa, ''Ina nuna jinkai ga wanda zan yi wa jinkai, zan ji tausayi ga wanda zan tausaya masa.''
16 so, then — not of him who is willing, nor of him who is running, but of God who is doing kindness:
Saboda haka, ba don wanda ke da aniya ba ne, ko kuwa wanda yake kokari ba, amma saboda Allah mai nuna jinkai.
17 for the Writing saith to Pharaoh — 'For this very thing I did raise thee up, that I might shew in thee My power, and that My name might be declared in all the land;'
Gama nassi ya ce da Fir'auna, '' Saboda wannan dalilin ne, na tada kai, don in nuna ikona mai karfi a kanka, don sunana ya yadu ga dukkan duniya.''
18 so, then, to whom He willeth, He doth kindness, and to whom He willeth, He doth harden.
Ta haka Allah ya nuna jinkansa ga wanda ya so, ya taurarar da zuciyar wanda ya ga dama.
19 Thou wilt say, then, to me, 'Why yet doth He find fault? for His counsel who hath resisted?'
Za kuce mani, to don me, ''Yake kama mu da llaifi? Wa ya taba yin jayayya da nufinsa?''
20 nay, but, O man, who art thou that art answering again to God? shall the thing formed say to Him who did form [it], Why me didst thou make thus?
In ma mun duba, kai mutum wanene kai da zaka ja da Allah? Ko abin da aka gina zai ce wa magininsa, ''Don me yasa ka ginani haka?''
21 hath not the potter authority over the clay, out of the same lump to make the one vessel to honour, and the one to dishonour?
Ko maginin ba shi da iko akan yimbu daya da zai gina tukunya mai daraja, wata kuma tukunyar don kowanne irin aiki?
22 And if God, willing to shew the wrath and to make known His power, did endure, in much long suffering, vessels of wrath fitted for destruction,
In ace Allah, dake niyyar nuna fushinsa da ikonsa, ya sanu, sai ya jure da matukar hakuri mai yawa da tukwanen fushi da ya shirya don hallakarwar fa?
23 and that He might make known the riches of His glory on vessels of kindness, that He before prepared for glory, whom also He did call — us —
To ko ma ya yi haka don ya nuna yalwar daukakarsa da take dauke da alheri, wanda ya shirya don daukakarsa tun farko?
24 not only out of Jews, but also out of nations,
Zai yiwu ma ya yi haka ne domin mu, mu da ya kira, ba ma daga cikin Yahudawa kadai ba, amma har ma daga cikin al'ummai?
25 as also in Hosea He saith, 'I will call what [is] not My people — My people; and her not beloved — Beloved,
Kamar yadda ya ce a cikin littafin Yusha'u: ''zan kira wadanda ba mutanena ba mutanena, da kuma kaunatattunta wadanda ba kaunatattu ba.
26 and it shall be — in the place where it was said to them, Ye [are] not My people; there they shall be called sons of the living God.'
Zai zama kuma a inda aka ce da su, “ku ba mutanena bane, za a kisa su 'ya'yan Allah mai rai.”'
27 And Isaiah doth cry concerning Israel, 'If the number of the sons of Israel may be as the sand of the sea, the remnant shall be saved;
Ishaya ya yi kira game da Isra'ila, ''in a ce yawan 'ya'yan Isra'ila zasu zama kamar yashi a bakin teku, ragowarsu ne kawai za su sami ceto.
28 for a matter He is finishing, and is cutting short in righteousness, because a matter cut short will the Lord do upon the land.
Ubangiji zai tabbatar da cikar kalmarsa a duniya, ba kuwa da dadewa ba.
29 and according as Isaiah saith before, 'Except the Lord of Sabaoth did leave to us a seed, as Sodom we had become, and as Gomorrah we had been made like.'
Yadda Ishaya ya rubuta ada, ''In da ba Ubangiji mai runduna bai bar mana zuriya ba, da zamu zama kamar Saduma, da kuma an maida mu kamar Gomarata.
30 What, then, shall we say? that nations who are not pursuing righteousness did attain to righteousness, and righteousness that [is] of faith,
To me za mu ce kenan? Ko al'ummai, da ba sa neman adalci, sun samu adalci ta wurin bangaskiya.
31 and Israel, pursuing a law of righteousness, at a law of righteousness did not arrive;
Amma Isra'ila, wadanda suka nemi adalcinsu ta wurin shari'a, ba su kai ga gaci ba.
32 wherefore? because — not by faith, but as by works of law; for they did stumble at the stone of stumbling,
To don me? don ba su neme shi da bangaskiya ba, amma ta ayyuka. Sun yi tuntube a kan dutse da zai sa laifi.
33 according as it hath been written, 'Lo, I place in Sion a stone of stumbling and a rock of offence; and every one who is believing thereon shall not be ashamed.'
Kamar yadda aka rubuta, “Ga, shi na ajiye dutse a kan Sihiyona dutsen tuntube mai sa laifi. Ga wanda ya bada gaskiya gare shi ba zai ji kunya ba.”

< Romans 9 >