< Revelation 6 >
1 And I saw when the Lamb opened one of the seals, and I heard one of the four living creatures saying, as it were a voice of thunder, 'Come and behold!'
Na duba lokacin da Dan Ragon ya bude daya daga cikin hatiman bakwai, sai na ji daya daga cikin rayayyun halittattun hudu ya fada da murya kamar tsawa, ''Zo!”
2 and I saw, and lo, a white horse, and he who is sitting upon it is having a bow, and there was given to him a crown, and he went forth overcoming, and that he may overcome.
Sai Na duba sai ga wani farin doki, mahayinsa na rike da baka, kuma an bashi rawani. Ya fito a matsayin mai nasara domin ya yi nasara.
3 And when he opened the second seal, I heard the second living creature saying, 'Come and behold!'
Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na biyu, sai na ji rayayyen halitta na biyu ya ce, ''Zo!''
4 and there went forth another horse — red, and to him who is sitting upon it, there was given to him to take the peace from the land, and that one another they may slay, and there was given to him a great sword.
Sai wani doki ya fito waje - jawur. Ga mahayin aka bashi dama ya dauke salama daga duniya, domin mutanen ta su karkashe juna. Wannan mahayin an bashi babbar takobi.
5 And when he opened the third seal, I heard the third living creature saying, 'Come and behold!' and I saw, and lo, a black horse, and he who is sitting upon it is having a balance in his hand,
Sa'anda Dan Ragon ya bude hatimi na uku, sai na ji rayayyen halita na uku ya ce, ''Zo!'' Na ga bakin doki, mai hawanta na rike da ma'auni a cikin hannunsa.
6 and I heard a voice in the midst of the four living creatures saying, 'A measure of wheat for a denary, and three measures of barley for a denary,' and 'The oil and the wine thou mayest not injure.'
Sai na ji kamar wata murya daga cikin rayayyun halittattun nan hudu ta ce, “Mudun alkama guda a kan albashin yini, kuma mudun sha'ir uku. Amma kar ka bata mai da kuma ruwan inabi.”
7 And when he opened the fourth seal, I heard the voice of the fourth living creature saying, 'Come and behold!'
Da Dan Ragon ya bude hatimi na hudu, na ji muryar rayayyen halitta na hudu ya ce, ''Zo!''
8 and I saw, and lo, a pale horse, and he who is sitting upon him — his name is Death, and Hades doth follow with him, and there was given to them authority to kill, (over the fourth part of the land, ) with sword, and with hunger, and with death, and by the beasts of the land. (Hadēs )
Sai na ga wani doki ruwan toka. Mai hawansa an bashi suna mutuwa, hades kuma tana biye da shi. An basu iko bisa kashi hudu na duniya su kashe da takobi, yunwa, cututtuka, da kuma namomin jeji na duniya. (Hadēs )
9 And when he opened the fifth seal, I saw under the altar the souls of those slain because of the word of God, and because of the testimony that they held,
Da Dan Ragon ya bude hatimi na biyar, a karkashin bagadi sai na ga rayukan wadanda aka kashe saboda maganar Allah, da kuma shaidar da suka rike.
10 and they were crying with a great voice, saying, 'Till when, O Master, the Holy and the True, dost Thou not judge and take vengeance of our blood from those dwelling upon the land?'
Suka yi kuka da babban murya, ''Sai yaushe ya mai iko duka, Mai Tsarki da gaskiya, zaka shari'anta mazaunan duniya, ka kuma dauki fansar jininmu?
11 and there was given to each one white robes, and it was said to them that they may rest themselves yet a little time, till may be fulfilled also their fellow-servants and their brethren, who are about to be killed — even as they.
Sai kowanne dayan su aka bashi farar tufa aka kuma fada masu su kara jira na lokaci kadan har sai adadin abokan bautar su da kuma 'yan'uwansu maza da mata wadanda aka kashe ya cika, kamar yadda aka kashe su.
12 And I saw when he opened the sixth seal, and lo, a great earthquake came, and the sun became black as sackcloth of hair, and the moon became as blood,
Da Dan Ragon ya bude hatimi na shidan, ina kallo sai ga babbar girgizar kasa. Rana ta zama baki kirin kamar bakar tufa, wata kuma ya zama kamar jini.
13 and the stars of the heaven fell to the earth — as a fig-tree doth cast her winter figs, by a great wind being shaken —
Taurarin sama suka fado kasa, kamar yadda itacen baure ke karkade 'ya'yansa da basu nuna ba, yayin da babbar iska ta kada.
14 and heaven departed as a scroll rolled up, and every mountain and island — out of their places they were moved;
Sama kuma ta bace kamar takardar da aka nannade. Kowanne dutse da tsibiri aka kau da shi daga wurinsa.
15 and the kings of the earth, and the great men, and the rich, and the chiefs of thousands, and the mighty, and every servant, and every freeman, hid themselves in the dens, and in the rocks of the mountains,
Sai sarakan duniya da muhimman mutane da sarakunan yaki, attajirai, da masu iko, tare da kowanne mutum, bawa da 'yantacce suka boye cikin duwatsu da tsaunuka.
16 and they say to the mountains and to the rocks, 'Fall upon us, and hide us from the face of Him who is sitting upon the throne, and from the anger of the Lamb,'
Suka ce wa tsaunuka da duwatsu, “Ku fado bisan mu! Ku boye mu daga fuskar wanda yake zaune bisa kursiyin da kuma fushin Dan Ragon.
17 because come did the great day of His anger, and who is able to stand?
Domin babban ranar fushin sa ta zo. Wa zai iya tsayawa?''