< Revelation 16 >

1 And I heard a great voice out of the sanctuary saying to the seven messengers, 'Go away, and pour out the vials of the wrath of God to the earth;'
Na ji babban murya na kira daga cikin haikali tana ce wa malai'iku bakwai, ''Ku je ku zuba tasoshi bakwai na fushin Allah a kan duniya.”
2 and the first did go away, and did pour out his vial upon the land, and there came a sore — bad and grievous — to men, those having the mark of the beast, and those bowing to his image.
Mala'ika na fari ya je ya zuba tasarsa a kan duniya; munanan gyambuna masu zafi suka fito wa mutane wadanda suke da alamar dabbar, wadanda suka bauta wa siffarsa.
3 And the second messenger did pour out his vial to the sea, and there came blood as of [one] dead, and every living soul died in the sea.
Mala'ika na biyu ya zuba tasarsa cikin teku. Ya zama jini, kamar jinin wanda ya mutu, kuma kowane abu mai rai da ke cikin tekun ya mutu.'
4 And the third messenger did pour out his vial to the rivers, and to the fountains of the waters, and there came blood,
Malaika na uku ya zuba tasarsa a cikin rafuffuka da mabulbulan ruwa, sai suka zama jini.
5 and I heard the messenger of the waters, saying, 'righteous, O Lord, art Thou, who art, and who wast, and who shalt be, because these things Thou didst judge,
Na ji mala'ikan ruwaye ya ce, ''Kai mai adalci ne - wanda ya ke yanzu wanda yake kuma a da, Mai Tsarkin nan, domin ka shari'anta wadannan abubuwa.
6 because blood of saints and prophets they did pour out, and blood to them Thou didst give to drink, for they are worthy;'
Domin sun zubar da jinin masu ba da gaskiya da annabawa, ka basu jini su sha; shine abinda da ya dace da su.
7 and I heard another out of the altar, saying, 'Yes, Lord God, the Almighty, true and righteous [are] Thy judgments.'
Na ji bagadi ya amsa, ''I, Ubangiji Allah Mai iko duka, shari'un ka gaskiya ne da adalci.''
8 And the fourth messenger did pour out his vial upon the sun, and there was given to him to scorch men with fire,
Mala'ika na hudu ya zuba tasarsa a kan rana, kuma aka ba shi izini ya kone jama'a da wuta.
9 and men were scorched with great heat, and they did speak evil of the name of God, who hath authority over these plagues, and they did not reform — to give to Him glory.
Suka kone da zafi mai tsanani, kuma suka sabi sunan Allah, wanda ke da iko akan annobai. Ba su tuba ba ko su daukaka shi.
10 And the fifth messenger did pour out his vial upon the throne of the beast, and his kingdom did become darkened, and they were gnawing their tongues from the pain,
Sai malaika na biyar ya zuba tasarsa a kan kursiyin dabban, sai duhu ya rufe mulkinsa. Suka cicciji harsunansu saboda zafi.
11 and they did speak evil of the God of the heaven, from their pains, and from their sores, and they did not reform from their works.
Suka yi sabon Allah na sama domin zafi da gyambunansu, suka kuma ki su tuba daga abin da suka yi.
12 And the sixth messenger did pour out his vial upon the great river, the Euphrates, and dried up was its water, that the way of the kings who are from the rising of the sun may be made ready;
Mala'ika na shida ya zuba tasarsa cikin babban rafi, Yufiretis. Ruwansa ya bushe domin a shirya hanya da sarakuna za su zo daga gabas.
13 and I saw [come] out of the mouth of the dragon, and out of the mouth of the beast, and out of the mouth of the false prophet, three unclean spirits like frogs —
Na ga kazamun ruhohi uku suna kama da kwadin da ke fitowa daga bakin diragon, da makaryacin annabi.
14 for they are spirits of demons, doing signs — which go forth unto the kings of the earth, and of the whole world, to bring them together to the battle of that great day of God the Almighty; —
Gama su ruhohin aljanu ne masu aikata alamun ban mamaki. Sun fita za su wurin sarakunan dukan duniya domin su tattaro su wuri daya saboda yaki a babbar ranar Allah Mai iko duka.
15 'lo, I do come as a thief; happy [is] he who is watching, and keeping his garments, that he may not walk naked, and they may see his unseemliness,' —
(''Duba! Ina zuwa kamar barawo! Mai albarka ne wanda ke zaune a fadake, wanda ke sanye da tufafinsa domin ba zai fita tsirara a ga tsiraicin sa ba.”)
16 and they did bring them together to the place that is called in Hebrew Armageddon.
Aka kawo su tare a wurin da ake kira Armagiddon da Ibraniyanci.
17 And the seventh messenger did pour out his vial to the air, and there came forth a great voice from the sanctuary of the heaven, from the throne, saying, 'It hath come!'
Mala'ika na bakwai ya zuba tasarsa cikin iska. Sa'annan babbar murya ta fito daga cikin haikali da kuma kursiyin, cewa, ''An gama!''
18 and there came voices, and thunders, and lightnings; and a great earthquake came, such as came not since men came upon the earth, so mighty an earthquake — so great!
Aka yi walkiya, da kararraki masu tsanani, da aradu da babbar girgizar kasa - girgizar da ta fi kowacce da aka taba yi tun da 'yan adam suke a duniya, girgizar da girma ta ke.
19 And it came — the great city — into three parts, and the cities of the nations did fall, and Babylon the great was remembered before God, to give to her the cup of the wine of the wrath of His anger,
Babban birnin ya rabu kashi uku, kuma biranen al'ummai suka fadi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, sai ya ba wancan birnin koko cike da ruwan innabi wanda aka yi daga fushinsa mai tsanani.
20 and every island did flee away, and mountains were not found,
Kowanne tsibiri ya bace, sai ba a kara ganin duwatsun ba.
21 and great hail (as of talent weight) doth come down out of the heaven upon men, and men did speak evil of God because of the plague of the hail, because its plague is very great.
Manyan duwatsun kankara, masu nauyin talanti, suka fado daga sama kan mutane. Suka zagi Allah domin annobar kankarar saboda annobar ta yi tsanani.

< Revelation 16 >