< Psalms 9 >
1 To the Overseer, 'On the Death of Labben.' — A Psalm of David. I confess, O Jehovah, with all my heart, I recount all Thy wonders,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2 I rejoice and exult in Thee, I praise Thy Name, O Most High.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3 In mine enemies turning backward, they stumble and perish from Thy face.
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4 For Thou hast done my judgment and my right. Thou hast sat on a throne, A judge of righteousness.
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5 Thou hast rebuked nations, Thou hast destroyed the wicked, Their name Thou hast blotted out to the age and for ever.
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6 O thou Enemy, Finished have been destructions for ever, As to cities thou hast plucked up, Perished hath their memorial with them.
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7 And Jehovah to the age abideth, He is preparing for judgment His throne.
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8 And He judgeth the world in righteousness, He judgeth the peoples in uprightness.
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9 And Jehovah is a tower for the bruised, A tower for times of adversity.
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10 They trust in Thee who do know Thy name, For Thou hast not forsaken Those seeking Thee, O Jehovah.
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11 Sing ye praise to Jehovah, inhabiting Zion, Declare ye among the peoples His acts,
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12 For He who is seeking for blood Them hath remembered, He hath not forgotten the cry of the afflicted.
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
13 Favour me, O Jehovah, See mine affliction by those hating me, Thou who liftest me up from the gates of death,
Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
14 So that I recount all Thy praise, In the gates of the daughter of Zion. I rejoice on Thy salvation.
don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
15 Sunk have nations in a pit they made, In a net that they hid hath their foot been captured.
Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
16 Jehovah hath been known, Judgment He hath done, By a work of his hands Hath the wicked been snared. (Meditation, Selah)
An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
17 The wicked do turn back to Sheol, All nations forgetting God. (Sheol )
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
18 For not for ever is the needy forgotten, The hope of the humble lost to the age.
Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
19 Rise, O Jehovah, let not man be strong, Let nations be judged before Thy face.
Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
20 Appoint, O Jehovah, a director to them, Let nations know they [are] men! (Selah)
Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)