< Psalms 77 >

1 To the Overseer, for Jeduthun. — A Psalm of Asaph. My voice [is] to God, and I cry, my voice [is] to God, And He hath given ear unto me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 In a day of my distress the Lord I sought, My hand by night hath been spread out, And it doth not cease, My soul hath refused to be comforted.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I remember God, and make a noise, I meditate, and feeble is my spirit. (Selah)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Thou hast taken hold of the watches of mine eyes, I have been moved, and I speak not.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I have reckoned the days of old, The years of the ages.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 I remember my music in the night, With my heart I meditate, and my spirit doth search diligently:
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 To the ages doth the Lord cast off? Doth He add to be pleased no more?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Hath His kindness ceased for ever? The saying failed to all generations?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Hath God forgotten [His] favours? Hath He shut up in anger His mercies? (Selah)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 And I say: 'My weakness is, The changes of the right hand of the Most High.'
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 I mention the doings of Jah, For I remember of old Thy wonders,
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 And I have meditated on all Thy working, And I talk concerning Thy doings.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 O God, in holiness [is] Thy way, Who [is] a great god like God?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Thou [art] the God doing wonders. Thou hast made known among the peoples Thy strength,
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 Thou hast redeemed with strength Thy people, The sons of Jacob and Joseph. (Selah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 The waters have seen Thee, O God, The waters have seen Thee, They are afraid — also depths are troubled.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 Poured out waters have thick clouds, The skies have given forth a noise, Also — Thine arrows go up and down.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 The voice of Thy thunder [is] in the spheres, Lightnings have lightened the world, The earth hath trembled, yea, it shaketh.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 In the sea [is] Thy way, And Thy paths [are] in many waters, And Thy tracks have not been known.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Thou hast led as a flock Thy people, By the hand of Moses and Aaron!
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.

< Psalms 77 >