< Psalms 69 >

1 To the Overseer. — 'On the Lilies,' by David. Save me, O God, for come have waters unto the soul.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 I have sunk in deep mire, And there is no standing, I have come into the depths of the waters, And a flood hath overflown me.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 I have been wearied with my calling, Burnt hath been my throat, Consumed have been mine eyes, waiting for my God.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Those hating me without cause Have been more than the hairs of my head, Mighty have been my destroyers, My lying enemies, That which I took not away — I bring back.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 O God, Thou — Thou hast known Concerning my overturn, And my desolations from Thee have not been hid.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Let not those waiting on Thee be ashamed because of me, O Lord, Jehovah of Hosts, Let not those seeking Thee Blush because of me, O God of Israel.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 For because of Thee I have borne reproach, Shame hath covered my face.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 A stranger I have been to my brother, And a foreigner to sons of my mother.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 For zeal for Thy house hath consumed me, And the reproaches of Thy reproachers Have fallen upon me.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 And I weep in the fasting of my soul, And it is for a reproach to me.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 And I make my clothing sackcloth, And I am to them for a simile.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Those sitting at the gate meditate concerning me, And those drinking strong drink, Play on instruments.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 And I — my prayer [is] to Thee, O Jehovah, A time of good pleasure, O God, In the abundance of Thy kindness, Answer me in the truth of Thy salvation.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Deliver me from the mire, and let me not sink, Let me be delivered from those hating me, And from deep places of waters.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 Let not a flood of waters overflow me, Nor let the deep swallow me up, Nor let the pit shut her mouth upon me.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Answer me, O Jehovah, for good [is] Thy kindness, According to the abundance Of Thy mercies turn Thou unto me,
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 And hide not Thy face from Thy servant, For I am in distress — haste, answer me.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Be near unto my soul — redeem it, Because of mine enemies ransom me.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Thou — Thou hast known my reproach, And my shame, and my blushing, Before Thee [are] all mine adversaries.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 Reproach hath broken my heart, and I am sick, And I look for a bemoaner, and there is none, And for comforters, and I have found none.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 And they give for my food gall, And for my thirst cause me to drink vinegar.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 Their table before them is for a snare, And for a recompence — for a trap.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Darkened are their eyes from seeing, And their loins continually shake Thou.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Pour upon them Thine indignation, And the fierceness of Thine anger doth seize them.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 Their tower is desolated, In their tents there is no dweller.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 For they have pursued him Thou hast smitten, And recount of the pain of Thy pierced ones.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Give punishment for their iniquity, And they enter not into Thy righteousness.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 They are blotted out of the book of life, And with the righteous are not written.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 And I [am] afflicted and pained, Thy salvation, O God, doth set me on high.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 I praise the name of God with a song, And I magnify Him with thanksgiving,
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 And it is better to Jehovah than an ox, A bullock — horned — hoofed.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 The humble have seen — they rejoice, Ye who seek God — and your heart liveth.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 For Jehovah hearkeneth unto the needy, And His bound ones He hath not despised.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 The heavens and earth do praise Him, Seas, and every moving thing in them.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 For God doth save Zion, And doth build the cities of Judah, And they have dwelt there, and possess it.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 And the seed of His servants inherit it, And those loving His name dwell in it!
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Psalms 69 >