< Psalms 44 >

1 To the Overseer. — By sons of Korah. An Instruction. O God, with our ears we have heard, Our fathers have recounted to us, The work Thou didst work in their days, In the days of old.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Thou, [with] Thy hand, nations hast dispossessed. And Thou dost plant them. Thou afflictest peoples, and sendest them away.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 For, not by their sword Possessed they the land, And their arm gave not salvation to them, But Thy right hand, and Thine arm, And the light of Thy countenance, Because Thou hadst accepted them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Thou [art] He, my king, O God, Command the deliverances of Jacob.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 By Thee our adversaries we do push, By Thy name tread down our withstanders,
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 For, not in my bow do I trust, And my sword doth not save me.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 For Thou hast saved us from our adversaries, And those hating us Thou hast put to shame.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 In God we have boasted all the day, And Thy name to the age we thank. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 In anger Thou hast cast off and causest us to blush, And goest not forth with our hosts.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Thou causest us to turn backward from an adversary, And those hating us, Have spoiled for themselves.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Thou makest us food like sheep, And among nations Thou hast scattered us.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Thou sellest Thy people — without wealth, And hast not become great by their price.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Thou makest us a reproach to our neighbours, A scorn and a reproach to our surrounders.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Thou makest us a simile among nations, A shaking of the head among peoples.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 All the day my confusion [is] before me, And the shame of my face hath covered me.
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 Because of the voice of a reproacher and reviler, Because of an enemy and a self-avenger.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All this met us, and we did not forget Thee, Nor have we dealt falsely in Thy covenant.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 We turn not backward our heart, Nor turn aside doth our step from Thy path.
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 But Thou hast smitten us in a place of dragons, And dost cover us over with death-shade.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If we have forgotten the name of our God, And spread our hands to a strange God,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Doth not God search out this? For He knoweth the secrets of the heart.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Surely, for Thy sake we have been slain all the day, Reckoned as sheep of the slaughter.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Stir up — why dost Thou sleep, O Lord? Awake, cast us not off for ever.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why Thy face hidest Thou? Thou forgettest our afflictions and our oppression,
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 For bowed to the dust hath our soul, Cleaved to the earth hath our belly.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Arise, a help to us, And ransom us for thy kindness' sake.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Psalms 44 >