< Psalms 35 >

1 By David. Strive, Jehovah, with my strivers, fight with my fighters,
Ta Dawuda. Yi hamayya, ya Ubangiji, da waɗanda suke hamayya da ni; yi faɗa da waɗanda suke faɗa da ni.
2 Take hold of shield and buckler, and rise for my help,
Ka ɗauki garkuwa da kuma makami; ka tashi ka taimake ni.
3 And draw out spear and lance, To meet my pursuers. Say to my soul, 'Thy salvation I [am].'
Ka ɗaga māshi da kuma abin da ake jefa a kan waɗanda suke fafarata. Ka ce wa raina, “Ni ne cetonka.”
4 They are ashamed and blush, those seeking my soul, Turned backward and confounded, Those devising my evil.
Bari waɗanda suke neman raina su sha kunya a kuma kunyatar da su; bari waɗanda suke shirya lalacewata su juya da baya su ruɗe.
5 They are as chaff before wind, And a messenger of Jehovah driving away.
Bari su zama kamar yayi a gaban iska, mala’ikan Ubangiji kuma yana korarsu;
6 Their way is darkness and slipperiness, And a messenger of Jehovah their pursuer.
bari hanyarsu tă yi duhu ta kuma yi santsi, mala’ikan Ubangiji kuma yana fafararsu.
7 For without cause they hid for me their netpit, Without cause they digged for my soul.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
8 Meet him doth desolation — he knoweth not, And his net that he hid catcheth him, For desolation he falleth into it.
bari lalaci yă kama su ba zato, bari tarkon da suka ɓoye yă kama su, bari su fāɗa cikin ramin, yă kai ga lalacinsu.
9 And my soul is joyful in Jehovah, It rejoiceth in His salvation.
Sa’an nan raina zai cika da farin ciki a cikin Ubangiji in yi kuma murna a cikin cetonsa.
10 All my bones say, 'Jehovah, who is like Thee, Delivering the poor from the stronger than he, And the poor and needy from his plunderer.'
Dukan raina zai ce, “Wane ne kamar ka, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da matalauta daga waɗanda suka fi ƙarfinsu, matalauta da masu bukata daga waɗanda suke musu fashi.”
11 Violent witnesses rise up, That which I have not known they ask me.
Shaidu marasa imani sun fito; suna mini tambaya a kan abubuwan da ban san kome a kai ba.
12 They pay me evil for good, bereaving my soul,
Suna sāka alherin da na yi musu da mugunta suka bar raina da nadama.
13 And I — in their sickness my clothing [is] sackcloth, I have humbled with fastings my soul, And my prayer unto my bosom returneth.
Duk da haka sa’ad da suke ciwo, na sanya rigar makoki na ƙasƙantar da kaina da azumi. Sa’ad da aka mayar mini da addu’o’i babu amsa,
14 As [if] a friend, as [if] my brother, I walked habitually, As a mourner for a mother, Mourning I have bowed down.
nakan yi ta yawo ina makoki sai ka ce yadda nake yi wa abokina ko ɗan’uwana. Nakan sunkuyar da kaina cikin baƙin ciki sai ka ce ina kuka domin mahaifiyata.
15 And — in my halting they have rejoiced, And have been gathered together, Gathered against me were the smiters, And I have not known, They have rent, and they have not ceased;
Amma sa’ad da na yi tuntuɓe, sukan taru suna murna; masu kai hari sun taru a kaina sa’ad da ban sani ba. Suna ɓata mini suna ba tsagaitawa.
16 With profane ones, mockers in feasts, Gnashing against me their teeth.
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17 Lord, how long dost thou behold? Keep back my soul from their desolations, From young lions my only one.
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18 I thank Thee in a great assembly, Among a mighty people I praise Thee.
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.
19 Mine enemies rejoice not over me [with] falsehood, Those hating me without cause wink the eye.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
20 For they speak not peace, And against the quiet of the land, Deceitful words they devise,
Ba sa maganar salama sukan ƙirƙiro zage-zagen ƙarya a kan waɗanda suka zama shiru a ƙasar.
21 And they enlarge against me their mouth, They said, 'Aha, aha, our eye hath seen.'
Sukan wage mini bakinsu suna cewa, “Allah yă ƙara! Da idanunmu mun gani.”
22 Thou hast seen, O Jehovah, Be not silent, O Lord — be not far from me,
Ya Ubangiji, ka ga wannan; kada ka yi shiru. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji.
23 Stir up, and wake to my judgment, My God, and my Lord, to my plea.
Ka farka, ka kuma tashi ka kāre ni! Ka yi mini faɗa, ya Allahna da shugabana.
24 Judge me according to Thy righteousness, O Jehovah my God, And they do not rejoice over me.
Ka nuna ni marar laifi ne ciki adalcinka, Ya Ubangiji Allahna; kada ka bari su yi farin ciki a kaina.
25 They do not say in their heart, 'Aha, our desire.' They do not say, 'We swallowed him up.'
Kada ka bari su ce wa kansu, “Allah yă ƙara, dā ma abin da mun so ke nan!” Ko su ce, “Mun haɗiye shi.”
26 They are ashamed and confounded together, Who are rejoicing at my evil. They put on shame and confusion, Who are magnifying themselves against me.
Bari dukan waɗanda suke farin ciki a kaina a wahalata su sha kunya su kuma ruɗe; bari dukan waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni su sha kunya da wulaƙanci.
27 They sing and rejoice, who are desiring my righteousness, And they say continually, 'Jehovah is magnified, Who is desiring the peace of His servant.'
Bari waɗanda suke murna saboda nasarata su yi sowa don farin ciki da murna; bari kullum su riƙa cewa, “A ɗaukaka Ubangiji, wanda yake farin ciki da zaman lafiyar bawansa.”
28 And my tongue uttereth Thy righteousness, All the day Thy praise!
Harshena zai yi zancen adalcinka da kuma yabonka dukan yini.

< Psalms 35 >