< Proverbs 23 >
1 When thou sittest to eat with a ruler, Thou considerest diligently that which [is] before thee,
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 And thou hast put a knife to thy throat, If thou [art] a man of appetite.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Have no desire to his dainties, seeing it [is] lying food.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Labour not to make wealth, From thine own understanding cease, Dost thou cause thine eyes to fly upon it? Then it is not.
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 For wealth maketh to itself wings, As an eagle it flieth to the heavens.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Eat not the bread of an evil eye, And have no desire to his dainties,
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 For as he hath thought in his soul, so [is] he, 'Eat and drink,' saith he to thee, And his heart [is] not with thee.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 Thy morsel thou hast eaten thou dost vomit up, And hast marred thy words that [are] sweet.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 In the ears of a fool speak not, For he treadeth on the wisdom of thy words.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Remove not a border of olden times, And into fields of the fatherless enter not,
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 For their Redeemer [is] strong, He doth plead their cause with thee.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Bring in to instruction thy heart, And thine ear to sayings of knowledge.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Withhold not from a youth chastisement, When thou smitest him with a rod he dieth not.
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 Thou with a rod smitest him, And his soul from Sheol thou deliverest. (Sheol )
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol )
15 My son, if thy heart hath been wise, My heart rejoiceth, even mine,
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 And my reins exult when thy lips speak uprightly.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Let not thy heart be envious at sinners, But — in the fear of Jehovah all the day.
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 For, is there a posterity? Then thy hope is not cut off.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Hear thou, my son, and be wise, And make happy in the way thy heart,
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Be not thou among quaffers of wine, Among gluttonous ones of flesh,
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 For the quaffer and glutton become poor, And drowsiness clotheth with rags.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Hearken to thy father, who begat thee, And despise not thy mother when she hath become old.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Truth buy, and sell not, Wisdom, and instruction, and understanding,
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 The father of the righteous rejoiceth greatly, The begetter of the wise rejoiceth in him.
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Rejoice doth thy father and thy mother, Yea, she that bare thee is joyful.
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 Give, my son, thy heart to me, And let thine eyes watch my ways.
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 For a harlot [is] a deep ditch, And a strange woman [is] a strait pit.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 She also, as catching prey, lieth in wait, And the treacherous among men she increaseth.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Who hath woe? who hath sorrow? Who hath contentions? who hath plaint? Who hath wounds without cause? Who hath redness of eyes?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 Those tarrying by the wine, Those going in to search out mixed wine.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 See not wine when it showeth itself red, When it giveth in the cup its colour, It goeth up and down through the upright.
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 Its latter end — as a serpent it biteth, And as a basilisk it stingeth.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Thine eyes see strange women, And thy heart speaketh perverse things.
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 And thou hast been as one lying down in the heart of the sea, And as one lying down on the top of a mast.
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 'They smote me, I have not been sick, They beat me, I have not known. When I awake — I seek it yet again!'
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”