< Numbers 32 >

1 And much cattle hath been to the sons of Reuben and to the sons of Gad, very many; and they see the land of Jazer, and the land of Gilead, and lo, the place [is] a place [for] cattle;
Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
2 and the sons of Gad, and the sons of Reuben, come in and speak unto Moses, and unto Eleazar the priest, and unto the princes of the company, saying:
Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
3 'Ataroth, and Dibon, and Jazer, and Nimrah, and Heshbon, and Elealeh, and Shebam, and Nebo, and Beon —
“Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
4 the land which Jehovah hath smitten before the company of Israel, is a land for cattle, and thy servants have cattle.'
ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
5 And they say, 'If we have found grace in thine eyes, let this land be given to thy servants for a possession; cause us not to pass over the Jordan.'
Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
6 And Moses saith to the sons of Gad and to the sons of Reuben, 'Do your brethren go in to the battle, and ye — do ye sit here?
Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
7 and why discourage ye the heart of the sons of Israel from passing over unto the land which Jehovah hath given to them?
Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
8 'Thus did your fathers in my sending them from Kadesh-Barnea to see the land;
Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
9 and they go up unto the valley of Eshcol, and see the land, and discourage the heart of the sons of Israel so as not to go in unto the land which Jehovah hath given to them;
Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
10 and the anger of Jehovah burneth in that day, and He sweareth, saying,
A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
11 They do not see — the men who are coming up out of Egypt from a son of twenty years and upward — the ground which I have sworn to Abraham, to Isaac, and to Jacob, for they have not been fully after Me;
‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
12 save Caleb son of Jephunneh the Kenezite, and Joshua son of Nun, for they have been fully after Jehovah;
ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
13 and the anger of Jehovah burneth against Israel, and He causeth them to wander in the wilderness forty years, until the consumption of all the generation which is doing the evil thing in the eyes of Jehovah.
Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
14 'And lo, ye have risen in the stead of your fathers, an increase of men — sinners, to add yet to the fury of the anger of Jehovah toward Israel;
“Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
15 when ye turn back from after Him, then He hath added yet to leave him in the wilderness, and ye have done corruptly to all this people.'
In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
16 And they come nigh unto him, and say, 'Folds for the flock we build for our cattle here, and cities for our infants;
Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
17 and we — we are armed hasting before the sons of Israel till that we have brought them in unto their place; and our infants have dwelt in the cities of defence because of the inhabitants of the land;
Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
18 we do not turn back unto our houses till the sons of Israel have inherited each his inheritance,
Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
19 for we do not inherit with them beyond the Jordan and yonder, for our inheritance hath come unto us beyond the Jordan at the [sun] -rising.'
Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
20 And Moses saith unto them, 'If ye do this thing: if ye are armed before Jehovah for battle,
Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
21 and every armed one of you hath passed over the Jordan before Jehovah, till his dispossessing His enemies from before Him,
in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
22 and the land hath been subdued before Jehovah — then afterwards ye do turn back, and have been acquitted by Jehovah, and by Israel; and this land hath been to you for a possession before Jehovah.
to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
23 'And if ye do not so, lo, ye have sinned against Jehovah, and know ye your sin, that it doth find you;
“Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
24 build for yourselves cities for your infants, and folds for your flock, and that which is going out from your mouth do ye.'
Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
25 And the sons of Gad and the sons of Reuben speak unto Moses, saying, 'Thy servants do as my lord is commanding;
Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
26 our infants, our wives, our cattle, and all our beasts, are there in cities of Gilead,
’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
27 and thy servants pass over, every armed one of the host, before Jehovah, to battle, as my lord is saying.'
Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
28 And Moses commandeth concerning them Eleazar the priest, and Joshua son of Nun, and the heads of the fathers of the tribes of the sons of Israel;
Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
29 and Moses saith unto them, 'If the sons of Gad and the sons of Reuben pass over with you the Jordan, every one armed for battle, before Jehovah, and the land hath been subdued before you, then ye have given to them the land of Gilead for a possession;
ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
30 and if they do not pass over armed with you, then they have possessions in your midst in the land of Canaan.'
Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
31 And the sons of Gad and the sons of Reuben answer, saying, 'That which Jehovah hath spoken unto thy servants — so we do;
Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
32 we — we pass over armed before Jehovah [to] the land of Canaan, and with us [is] the possession of our inheritance beyond the Jordan.'
Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
33 And Moses giveth to them, to the sons of Gad, and to the sons of Reuben, and to the half of the tribe of Manasseh son of Joseph, the kingdom of Sihon king of the Amorite, and the kingdom of Og king of Bashan, the land by its cities, in the borders, the cities of the land round about.
Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
34 And the sons of Gad build Dihon, and Ataroth, and Aroer,
Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
35 and Atroth, Shophan, and Jaazer, and Jogbehah,
Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
36 and Beth-Nimrah, and Beth-Haran, cities of defence, and sheepfolds.
Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
37 And the sons of Reuben have build Heshbon, and Elealeh, and Kirjathaim,
Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
38 and Nebo, and Baal-Meon (changed in name), and Shibmah, and they call by [these] names the names of the cities which they have built.
haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
39 And sons of Machir son of Manasseh go to Gilead, and capture it, and dispossess the Amorite, who [is] in it;
Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
40 and Moses giveth Gilead to Machir son of Manasseh, and he dwelleth in it.
Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
41 And Jair son of Manasseh hath gone and captureth their towns, and calleth them 'Towns of Jair;'
Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
42 and Nobah hath gone and captureth Kenath, and its villages, and calleth it Nobah, by his own name.
Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.

< Numbers 32 >