< Numbers 31 >
1 And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 'Execute the vengeance of the sons of Israel against the Midianites — afterwards thou art gathered unto thy people.'
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 And Moses speaketh unto the people, saying, 'Be ye armed some of you for the host, and they are against Midian, to put the vengeance of Jehovah on Midian;
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4 a thousand for a tribe — a thousand for a tribe, to all the tribes of Israel — ye do send to the host.'
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5 And there are given out of the thousands of Israel a thousand for a tribe, twelve thousand armed ones of the host;
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6 and Moses sendeth them, a thousand for a tribe, to the host, them and Phinehas son of Eleazar the priest, to the host; and the holy vessels, and the trumpets of the shouting, in his hand.
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
7 And they war against Midian, as Jehovah hath commanded Moses, and slay every male;
Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
8 and the kings of Midian they have slain, besides their pierced ones, Evi, and Rekem, and Zur, and Hur, and Reba, five kings of Midian; and Balaam son of Beor, they have slain with the sword.
A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
9 And the sons of Israel take captive the women of Midian, and their infants; and all their cattle, and all their substance, and all their wealth they have plundered;
Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
10 and all their cities, with their habitations, and all their towers, they have burnt with fire.
Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
11 And they take all the spoil, and all the prey, among man and among beast;
Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
12 and they bring in, unto Moses, and unto Eleazar the priest, and unto the company of the sons of Israel, the captives, and the prey, and the spoil, unto the camp, unto the plains of Moab, which [are] by Jordan, [near] Jericho.
suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
13 And Moses, and Eleazar the priest, and all the princes of the company, go out to meet them, unto the outside of the camp,
Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
14 and Moses is wroth against the inspectors of the force, chiefs of the thousands, and chiefs of the hundreds, who are coming in from the host of the battle.
Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
15 And Moses saith unto them, 'Have ye kept alive every female?
Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
16 lo, they — they have been to the sons of Israel, through the word of Balaam, to cause a trespass against Jehovah in the matter of Peor, and the plague is in the company of Jehovah.
Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
17 'And now, slay ye every male among the infants, yea, every woman known of man by the lying of a male ye have slain;
Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
18 and all the infants among the women, who have not known the lying of a male, ye have kept alive for yourselves.
amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
19 'And ye, encamp ye at the outside of the camp seven days — any who hath slain a person, and any who hath come against a pierced one, ye cleanse yourselves on the third day, and on the seventh day — ye and your captives;
“Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
20 and every garment, and every skin vessel, and every work of goats' [hair], and every wooden vessel, ye yourselves cleanse.'
Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
21 And Eleazar the priest saith unto the men of the host who go in to battle, 'This [is] the statute of the law which Jehovah hath commanded Moses:
Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
22 only, the gold, and the silver, the brass, the iron, the tin, and the lead,
Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
23 every thing which may go into fire, ye cause to pass over through fire, and it hath been clean; only, with the water of separation it is cleansed, and all that may not go into fire, ye cause to pass over through water;
da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 and ye have washed your garments on the seventh day, and have been clean, and afterwards ye come in unto the camp.'
A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
25 And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
26 'Take up the sum of the prey of the captives, among man and among beast, thou, and Eleazar the priest, and the heads of the fathers of the company;
“Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
27 and thou hast halved the prey between those handling the battle who go out to the host and all the company;
Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
28 and thou hast raised a tribute to Jehovah from the men of war, who go out to the host, one body out of five hundred, of man, and of the herd, and of the asses, and of the flock;
Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
29 from their half ye do take, and thou hast given to Eleazar the priest — the heave-offering of Jehovah.
Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
30 'And from the sons of Israel's half thou dost take one possession out of fifty, of man, of the herd, of the asses, and of the flock, of all the cattle, and thou hast given them to the Levites keeping the charge of the tabernacle of Jehovah.'
Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
31 And Moses doth — Eleazar the priest also — as Jehovah hath commanded Moses.
Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
32 And the prey, the residue of the spoil which the people of the host have spoiled, is of the flock six hundred thousand, and seventy thousand, and five thousand;
Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
33 and of the herd two and seventy thousand;
shanu 72,000
34 and of asses one and sixty thousand;
da jakuna 61,000.
35 and of human beings — of the women who have not known the lying of a male — all the persons [are] two and thirty thousand.
Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
36 And the half — the portion of those who go out into the host — the number of the flock is three hundred thousand, and thirty thousand, and seven thousand and five hundred.
Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
37 And the tribute to Jehovah of the sheep is six hundred five and seventy;
tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
38 and the herd [is] six and thirty thousand, and their tribute to Jehovah [is] two and seventy;
shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
39 and the asses [are] thirty thousand and five hundred, and their tribute to Jehovah [is] one and sixty;
jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
40 and the human beings [are] sixteen thousand, and their tribute to Jehovah [is] two and thirty persons.
mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
41 And Moses giveth the tribute — Jehovah's heave-offering — to Eleazar the priest, as Jehovah hath commanded Moses.
Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
42 And of the sons of Israel's half, which Moses halved from the men who war —
Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
43 and the company's half is, of the flock three hundred thousand, and thirty thousand, seven thousand and five hundred;
kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
44 and of the herd six and thirty thousand;
shanu 36,000,
45 and of asses thirty thousand and five hundred;
jakuna 30,500
46 and of human beings sixteen thousand —
da mutane 16,000.
47 Moses taketh from the sons of Israel's half the one possession from the fifty, of man and of beast, and giveth them to the Levites keeping the charge of the tabernacle of Jehovah, as Jehovah hath commanded Moses.
Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
48 And the inspectors whom the thousands of the host hath, (heads of the thousands and heads of the hundreds), draw near unto Moses,
Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
49 and they say unto Moses, 'Thy servants have taken up the sum of the men of war who [are] with us, and not a man of us hath been missed;
suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
50 and we bring near Jehovah's offering, each that which he hath found, vessels of gold — chain, and bracelet, seal-ring, [ear] -ring, and bead — to make atonement for ourselves before Jehovah.'
Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
51 And Moses receiveth — Eleazar the priest also — the gold from them, every made vessel,
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
52 and all the gold of the heave-offering which they have lifted up to Jehovah is sixteen thousand seven hundred and fifty shekels, from heads of the thousands, and from heads of the hundreds;
Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
53 (the men of the host have spoiled each for himself);
Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
54 and Moses taketh — Eleazar the priest also — the gold from the heads of the thousands and of the hundreds, and they bring it in unto the tent of meeting — a memorial for the sons of Israel before Jehovah.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.