< Numbers 19 >
1 And Jehovah speaketh unto Moses, and unto Aaron, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 'This [is] a statute of the law which Jehovah hath commanded, saying, Speak unto the sons of Israel, and they bring unto thee a red cow, a perfect one, in which there is no blemish, on which no yoke hath gone up;
“Wannan ita ce ƙa’ida wadda Ubangiji ya umarta. Faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jan karsana marar lahani, ko marar aibi wadda ba a taɓa sa ta tă yi noma ba.
3 and ye have given it unto Eleazar the priest, and he hath brought it out unto the outside of the camp, and hath slaughtered it before him.
Ka ba wa Eleyazar firist; a kuma kai ta bayan sansani, a yanka a gaban Eleyazar.
4 'And Eleazar the priest hath taken of its blood with his finger, and hath sprinkled over-against the front of the tent of meeting of her blood seven times;
Sa’an nan Eleyazar firist zai ɗiba jininta a yatsarsa, yă yayyafa sau bakwai wajen gaban Tentin Sujada.
5 and [one] hath burnt the cow before his eyes; her skin, and her flesh, and her blood, besides her dung, he doth burn;
Sa’an nan a ƙone dukan karsanar, haɗe da fatarta, naman, jinin da kayan cikin, yayinda Eleyazar yake kallo.
6 and the priest hath taken cedar wood, and hyssop, and scarlet, and hath cast unto the midst of the burning of the cow;
Firist zai ɗauki itacen al’ul, da hizzob, da jan ulu, yă jefa su a kan karsanar da ake ƙonewa.
7 and the priest hath washed his garments, and hath bathed his flesh with water, and afterwards doth come in unto the camp, and the priest is unclean till the evening;
Bayan haka, dole firist yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka. Sa’an nan zai iya shiga cikin sansani, amma zai kasance da ƙazanta har yamma.
8 and he who is burning it doth wash his garments with water, and hath bathed his flesh with water, and is unclean till the evening.
Dole mutumin da ya ƙone ta yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka, shi ma zai kasance da ƙazanta har yamma.
9 'And a clean man hath gathered the ashes of the cow, and hath placed at the outside of the camp, in a clean place, and it hath become to the company of the sons of Israel a charge for waters of separation — it [is] a [cleansing];
“Mutumin da yake da tsarki, zai tara tokar karsanar, yă sa ta a wurin da yake da tsabta a bayan sansani. Jama’ar Isra’ilawa ne za su adana shi don amfani a ruwan tsabtaccewa; wannan domin tsarkakewa ne daga zunubi.
10 and he who is gathering the ashes of the heifer hath washed his garments, and is unclean till the evening; and it hath been to the sons of Israel, and to the sojourner who is sojourning in their midst, for a statute age-during.
Dole mutumin da ya tara tokar karsanar yă wanke rigunarsa, zai kuwa kasance da ƙazanta har yamma. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta har abada ga Isra’ilawa, da kuma baƙin da suke zama a cikinsu.
11 'He who is coming against the dead body of any man — is unclean seven days;
“Duk wanda ya taɓa gawa, zai kasance da ƙazanta har kwana bakwai.
12 he doth cleanse himself for it on the third day, and on the seventh day he is clean; and if he cleanse not himself on the third day, then on the seventh day he is not clean.
Dole yă tsarkake kansa da ruwa a rana ta uku, da kuma a rana ta bakwai; sa’an nan zai zama da tsarki. Amma in bai tsarkake kansa a rana ta uku da kuma a rana ta bakwai ba, ba zai kasance da tsarki ba.
13 Any one who is coming against the dead, against the body of man who dieth, and cleanseth not himself — the tabernacle of Jehovah he hath defiled, and that person hath been cut off from Israel, for water of separation is not sprinkled upon him; he is unclean; his uncleanness [is] still upon him.
Duk wanda ya taɓa gawar wani, bai kuma tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da tabanakul na Ubangiji ke nan. Dole a ware wannan mutum daga cikin Isra’ilawa. Gama ba a yayyafa ruwan tsabtaccewa a kansa ba; ya ƙazantu, ya kasance da ƙazanta ke nan.
14 'This [is] the law, when a man dieth in a tent: every one who is coming in unto the tent, and all that [is] in the tent, is unclean seven days;
“Ga ƙa’idar da za a bi in mutum ya mutu a cikin tenti. Duk wanda ya shiga tentin, kuma duk wanda yake cikinsa, za su zama da ƙazanta har kwana bakwai,
15 and every open vessel which hath no covering of thread upon it is unclean.
kuma kowane abin da ake zuba kaya, wanda ba shi da murfi a kansa, zai zama da ƙazanta.
16 'And every one who cometh, on the face of the field, against the pierced of a sword, or against the dead, or against a bone of man, or against a grave, is unclean seven days;
“Wanda duk yake a fili, ya kuma taɓa gawa wanda aka kashe da takobi, ko wanda ya mutu mutuwar Allah, ko ƙashin mutum, ko kabari, zai ƙazantu har bakwai.
17 and they have taken for the unclean person of the ashes of the burning of the [cleansing], and he hath put upon it running water unto a vessel;
“Ga wanda ya ƙazantu kuwa, a ɗiba toka daga hadaya ta ƙonawa ta tsarkakewa, a zuba a cikin tulu, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu a kansu.
18 and a clean person hath taken hyssop, and hath dipped [it] in water, and hath sprinkled on the tent, and on all the vessels, and on the persons who have been there, and on him who is coming against a bone, or against one pierced, or against the dead, or against a grave.
Sa’an nan wanda yake tsarkakakke, zai ɗauki hizzob yă tsoma a ruwa, yă yayyafa a tentin da dukan kayayyakinsa, da kuma a kan mutanen da suke wurin. Dole kuma yă yayyafa ruwan a kan duk wanda ya taɓa ƙashin mutu, ko kabari, ko kuma wanda aka kashe, ko wanda ya yi mutuwa ta Allah.
19 'And the clean hath sprinkled [it] on the unclean on the third day, and on the seventh day, and hath cleansed him on the seventh day, and he hath washed his garments, and hath bathed with water, and hath been clean in the evening.
A rana ta uku, da ta bakwai kuma mai tsarkakewa zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, a rana ta bakwai kuma yă tsarkake shi. Wanda aka tsarkaken kuwa, dole yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka da yamma, zai kuma tsarkaka.
20 'And the man who is unclean, and doth not cleanse himself, even that person hath been cut off from the midst of the assembly; for the sanctuary of Jehovah he hath defiled; water of separation is not sprinkled upon him; he [is] unclean.
Amma in wanda yake da ƙazanta bai tsarkake kansa ba, dole a ware shi daga cikin jama’a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Ubangiji. Ba a yayyafa masa ruwa na tsarkakewa ba, ya zama da ƙazanta.
21 'And it hath been to them for a statute age-during, that he who is sprinkling the water of separation doth wash his garments, and he who is coming against the water of separation is unclean till the evening,
Wannan za tă zama musu dawwammamiyar farilla. “Mutumin da ya yayyafa ruwa na tsarkakewa, shi ma dole yă wanke rigarsa. Duk wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa, zai kasance da ƙazanta har yamma.
22 and all against which the unclean person cometh is unclean, and the person who is coming against [it] is unclean till the evening.'
Duk abin da mai ƙazanta ya taɓa, ya ƙazantu, kowa kuma ya taɓa wannan abu, ya ƙazantu ke nan, har yamma.”